Rundunan yan sanda a jahar Adamawa ta tura jami anta domin ganin an sake zabuka lafiya.

Rundunan yan sandan jahar Adamawa tace ta kimtsa tsaf domin ganin an kammala zabe da za sake a wasu mazabu dake fadin jahar Adamawa. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar a yola. Sanarwa tace rundunan ta hada kai da takwarorinta domin daukan dukkanin matakai da suka dace domin ganin ba a samu tashin hankaliba a lokaci dama bayan zabe. Sanarwan ta kima kirayi all ummah jahar ta Adamawa da sukasance masu kai rahoton dukkanin abinda basu yarda da shiba tare kuma da baiwa hukumomin tsaro hadin kai da goyon baya domin ganin an kammal zaben lafiya. Harwayau sanarwa ta kara da cewa rundunan zata saka kafar wando daya da dukkanin wanda zaiyiwa doka karan tsaye. Don haka ya kamata a kaicewa duk abinda zai kawo tashin hankali a tsakanin al umma.

Comments

Popular posts from this blog

Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta taimakawa iyalain Jamin an yan sanda da suka gamu da ajalinsu a bakin aiki.

Police in Adamawa Arrestet 31 year for serial theft.

Jambutu got new Chairman of PCRC.