Rundunan yan sanda a jahar Adamawa ta tura jami anta domin ganin an sake zabuka lafiya.

Rundunan yan sandan jahar Adamawa tace ta kimtsa tsaf domin ganin an kammala zabe da za sake a wasu mazabu dake fadin jahar Adamawa. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar a yola. Sanarwa tace rundunan ta hada kai da takwarorinta domin daukan dukkanin matakai da suka dace domin ganin ba a samu tashin hankaliba a lokaci dama bayan zabe. Sanarwan ta kima kirayi all ummah jahar ta Adamawa da sukasance masu kai rahoton dukkanin abinda basu yarda da shiba tare kuma da baiwa hukumomin tsaro hadin kai da goyon baya domin ganin an kammal zaben lafiya. Harwayau sanarwa ta kara da cewa rundunan zata saka kafar wando daya da dukkanin wanda zaiyiwa doka karan tsaye. Don haka ya kamata a kaicewa duk abinda zai kawo tashin hankali a tsakanin al umma.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie