Yan sanda a jahar Adamawa sun samu nasaran kashe mutane uku da ake zargi masu garkuwa da mutane ne tare da ceto mutane biyu da akayi garkuwa da su.
Rundunan yan sandan jahar Adamawa tayi nasaran ceto mutane biyu tare da hallaka mutane uku da ake zargi masuyin garkuwa da mutane ne a tsaunin Koma daka wasu bangarorin kananan hukumomin Fufore da Jada a jahar Adamawa.
Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya baiyana haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola.
Sanarwan ta baiyana cewa rundunan karkashin rundunan dakile laifuka wato Crack tare da hadin gwiwar yan Kai, mafarauta, kungiyar Tabbital Pulaku inda sukayi diran mikiya a mabuyar masu garkuwa da mutane bayan sunyi dauki ba dadi da su ne dai hakan ya baiwa rundunan akawa da mutane uku kahira a yayinda wasu sun ranta ana kare da raunukan harbi a jikinsu, tare Kuma da ceto mutane biyu. Wadanda akayi garkuwa da su
A rana karaba da ta gabata ne dai wasu dauke da makamai dira gidan Alhaji Jibo Karlahi inda sukayi awun gaba da Umar Jibo dan shejarau 18 da Hassan mai shekaru 13 zuwa nabayarsu
Kwamishinan yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola ya yabawa kwamnadan Crack da Jami ansa da kungiyar Tabitak Pulaku dama mafarauta bisa na mijin kokari da suakyi na dakile aikata kaifuka a fadin jahar.
Kwamishinan ya Kuma kirayi daukacin Al ummar jahar ta Adamawa da sukasance suna taimakawa rundunan da wasu bayanai da zai taimakawa rundunan takawa masu tada zaune tsaye birki
Ya Kuma tabbatarwa gwamnatin jahar dama Al ummar jahar Adamawa cewa rundunan ta kimtsa tsaf domin tarwatsa masu aukaya kaifuka daga maboyarsu dake fadin jaha
rundunan ta kuma gano makamai a mabayar masu garkuwa da mutane tare da wasu kayaki.

Comments
Post a Comment