Majalisar dokokin jahar Gombe ta dakatar da zamanta sakamokon yajin aikin gargadi na kwanaki biyu da kungiyar kwadigo keyi na kasa baki Daya.
Rahotanni daga jahar Gimbe sun baiyana cewa yajin aikin gargadi na kwanaki biyu wanda kungiyar kwadigo N LC keyi a fadin kasan nan kungiyar a jiya ta murci majalisar dokokin jajar Gombe da ta dakatar da zamanta da zatayi domin tantance sabbin sunye kwamishinoni jahar da ka tura mata.
Hakan na kunshene a cikin wata takarda da hukumar gudanarwar majalisar ta fitar inda tace majalisar ta dakatar da zamanta ne biyo bayan yajin aikin hargadi na kwana biyu da kungiyar kwadigo ta shirya wanda aka fara daga ran 5 zuwa 6- 9-2023.
A rawaito cewa a safiya talatan nan ne dai majalisar ta shirya domin fara tantance sabbin mutane 17 a matsayin kwamiahinoni hakan yasa ala tilas majalisar ta dage zamanta domin yin mubaya a da yajin aikin gargadi da kungiyar kwadigo keyi na kwana biyu a fadan Najeriya.
Rahotanni na cewa akasarin aiyukan gwamnati ya tsaya cik a cikin garin Gombe harma da cibiyoyin masu zaman Kansu suma sun rurrufe domin nuna goyon bayansu ga kungiyar kwadigo da ta aiyana yajin aikin gargadi sakamokon cire tallafin maifetur da gwamnatin tarayya tayi.
Kuma anga jami an tsaro na sintiri tun daga lokacon da aka fara yajin aikin na kwana biyu.

Comments
Post a Comment