Gwamnan jahar Filatau ya jajantawa iyalen wadanda hatsarin wutan lantarki ya shafa a jahar.
Rahotanni daga Jahar Filatau na cewa gwamnan jahar Barista Caleb Manassah Mutfwang ya nuna alhininsa da jajantawa al umma karamar hukumar Jos ta arewa biyo bayan matsalar wutan lantarki da yayi sanadiyar rasa rayuka da kayaki a safiyar asabar din nan. Gwamnan wanda mataimakinsa Ngo Josephine piyo ya wakilceshi a ziayar da wakaiwa wadanda lamarin ya shafa a asibitin koyarwa na Jami ar Jos dake Ola inda ya nuna bakin cikinsa da akuwar lamarin tare dayiwa iyalen wadanda lamarin ya shafa da Allah ya bawa wadanda suka jikkata sauki ya kuma baiwa iyalen wadanda suka rasa yan uwansu jimre hakurin rashi da sukayi. Gwamnan ya kuma baiyana lamarin a matsayin abun takaicine kuma abun bakincikine don haka ya tabbatar da cewa gwamnati zatayi dukkanin maiyiwa domin bada kariya ga al umma dama yan kasuwa da kuma ganin irin wannan lamarin bai sake aukuwaba. Gwamnan Mutfwang yayi alkawarin cewa gwamnatinsa zata taimakwa iyalen ...