Naja'atu Muhammad; Dantakaran Gwamna a Jihar Gombe Na PDP Makaryaci Ne
Daga Abdullahi Tukur
Hajiya Naja'atu Muhammed ta sake jaddada aniyarta na cewa Dan takaran gwamna a karkashin tutar jam'iyar PDP a jahar Gombe Farfesa Isa Ali Pantami makaryacine.
Hajiya Naja atu ta baiyana hakane a hirarta da BMC Hausa inda tace Bata zauna da wasu ko Waniba dangane da ta bada hakuri, Kuma babu wata tawaga da sukazo ko ta tura da sunan zata bada hakuri ko ta janye kalamanta, ita bata san wannanba, saboda haka tananan kan bakanta na cewar Farfesa Pantami da mutanensa suna karya.
Dangane da jita jitan cewa wasu sunje da sunan wakilanta da su baiwa Pantami hakuri akan kalaman Hajiya Naja'atu tace bata tura kowaba Kuma basu gaya mataba, saboda haka suma sun zuba karya, don haka it kam ba ta janye kalaman nataba tananan daram akansu.
Hajiya Naja'atu, ta baiyana Pantami a matsayin munafuki, saboda haka ba gudu ba Ja dabaya akan wannan kalaman.
Hajiya Naja'atu Muhammed ta kara da cewar, kowa yana iya yin nashi karya don haka ita Kam ba wadanda ta tura don suje su bada hakuri, ko Kuma wasu suka sameta don ta bada hakuri.

Comments
Post a Comment