An yaba da kamun ludayin Shugaba Bola Tinubu cikin kwanaki dari dayayi akan mulki.
A yayinda shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya cika kwanaki dari akan Mulki shugabancin Najeriya an yaba da kamun ludayinsa duba da irin yanayin matsalar rayuwa da ake ciki. Alhaji Adam Hassan Ibrahim shugaban kungiyar yan kasuwa a Arewacin Najeriya ne ya baiyana haka a zantawarsa da jaridar Al Nur bayan godiya da yayiwa Allah madaukakin sarki yace shugaba Bola Tinubu ya taka rawan gani a fannoni daban daban a cikin kwanaki dari da yayi na farkon mulkinsa. Alhaji Adam Hassan yace shugaba Bola Tinubu ya fitar da tsare tsare da zasu kawo cigaban kasa musammanma a bangaren tattalin arziki da Kuma bunkasa harkokin noma da dai sauransu. Alhaji Hassan yace duk dacewa ana cikin wani yanayi da wahalar rayuwa Amman da yardan Allah komai zai daidaita domin kuwa a cewarsa bayan wahala akwai sauki. Ya kara dacewa ko a yanzu hakama shugaban kasa ya tafi kasar indiya domin halartan taron G ...