Posts

Showing posts from October, 2024

Wani matashi da ake zargin da yunkurin hallaka kansa ya shiga kamar Yan sanda a jahar Adamawa.

Image
  Hukumomin Yan sanda a jahar Adamawa yanzu haka tana tsare da wani matashi Mai Suna Abdullahi Muhammed Mai shekaru 30 da haifuwa Dan karamar hukumar Gashaka jahar Taraba. An kama matashin ne bisa zarginsa da hallaka kansa a karamar hukumar Mayo Belwa dake  jahar Adamawa, ana zargin matashin ne a lokacinda yayi yunkurin kama Tiransifoma Mai karfin 33kv dake tsakanin Yola zuwa Jalingo. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya baiyana haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola. Sanarwan ta Kuma baiyana cewa daga Jin labarin haka kwamishin yan sandan jahar Adamawa Dankwambo Morris ya umurci jami an  Yan sandan ofishin Yan sanda dake karamar hukumar Moyo Belwa da su garzaya wurin sai akayi Sa a aka sameshi Yana kokari hallaka kansa yanzu haka Yana hanun Yan sanda domin cigaba da bincike Kuma da zaran an kammala bincike za a gurfanar da shi a gaban kotu. Sanarwan ta Kuma baiyana cewa rundunan yan sandan a shirye take wajen kare rayuka dakum duki

Rundunan Yan sanda a jahar Adamawa ta lashi takwabin hukunta duk Wanda aka samu dayiwa doka Karan tsaye a lokacin bikin samun yanci.

Image
  Rundunan yan sandan jahar Adamawa tare da takwarorinta zasu daukai dukkanin mataki da suka dace domin dakile dukkanin masu yin amfani da bikin ranan yanci wajen zanga zanga saboda haka a shirye suke su shiga kafar wando Daya da duk wadanda keyiwa zaman lafiya Jahar barazana. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola. Sanarwan tace rundunan ta tunin da sanya ido tare da tura Jami anta wuwaren taruwar jama a domin ganin ko a kwai Wanda zai karya doka. Sanarwan ta kirayi Al umma da sukasance masu taimakawa hukumomin tsaro da wasu bayanain da zai taimaka wajen takawa masu yiwa zaman lafiya barazana birki.