Posts

Showing posts from May, 2023

Kamfanin Dangote zai cigaba da karfafa dankon zumunci a tsakaninsa da al ummomi dake kewaye dashi.

Image
Kamfanin Dangote ya kara jaddada a niyyar shi na na ci gaba da zaman lafiya da al'ummomi dake kewaye da shi. Babban Manajan kamfanin, Malam Bello Danmusa ne ya baiynana haka yayin zaman ganawa da masu ruwa da tsaki da ya wakana a garin Numan. Babban Manajan kamfanin, Malam Bello Danmusa yace gina kyakkyawan alaka da al'umomi dake kewaye da kamfanin abu ne wanda ya dauka da muhimmanci matuka shi yasa ma ta shirya wannan taron ganawar. Danmusa yace, kamfanin Dangote dake Numan na aiki tare da al'umomin dake kewaye da shi a fannonin ilimi da aiyukan tallafi ta hanyoyi daya tsara domin inganta rayuwan mutanen da ke yankin. A cewar shi, kamfanin Dangote zai ci gaba da ganawa da masu ruwa da tsakin domin yin hakan zai basu daman tattaunawa tare da bullo da hanyoyi da za a amfana, a kuma samu zaman lafiya tsakanin juna domin ci gaban kamfanin, al'ummomin, jaha dama kasa baki daya. Da yayi jawabi kan muhimmancin wannan zama, Babban Jami'in Ofishin hulda da al'u

An taya gwamna. Fintir murna.

Image
Alhaji Suleiman Yusuf Jami in tsare tsaren aikin hajji karamar hukumar Madagali a jahar Adamawa ya taya gwamna Ahmadu Umaru Finti murnan rantsar dashi a matsayin gwamna karo na biyu a jahar Adamawa. Akhaji Yusuf yace yayi farincikin ganin an kammal bikin rantsar da gwamnan lafiya ba tare da watamatsalaba kuma ya na mai fatan gwamnan zaicigaba da gudanar da aiyukan cigaban jahar dama inganta tsaro a fadin jahar baki daya. Ya kuma kirayi daukacin al ummar jahar ta Adamawa da sukasance masu baiwa gwamnan hadin kai da goyon baya domin ganin gwamnan ya samu damar gudanar fa aiyukan cigaban jahar baki daya.

Hukumar aikin hajji jahar Adamawa ta baiyana ranan da za a fara jigilan maniyatan jahar zuwa kasa mai tsarki.

Image
Hukumar aikin hajjin jahar Adamawa tace ta kammala dukkanin shirye shiryenta domin gudanar da aikin hajjin wannan shekara a kasa mai tsarki. Babban sakataren hukumar a jahar Adamawa Dr Salihu Abubakar ne yabaiyana haka a lokacin da yake jawabi a wurin rufe bita wanda hukumar ta shiryawa maniyata a yola. Dr Salihu Abubakar yaja hankalin maniyatan da sukasance a shirye domin hukumar ta kammala shirinta na fara tafiya kasa mai tsarki domin gudanar da aikin hajji. Shugaban hukumar ya kuma sanar da cewa za a fara jigilan maniyatan jahar Adamawa a ranan biyu ga watan shiddan wanan shekara. Shima a jawabinsa Jami in tsare tsaren aikin hajji karamar hukumar yola ta arewa Alhaji Ya u Gambo ya kirayi maniyatan da sukasance masuyin amfani da abunda suka koya a lokacinda ake yi musu bita domin ganin an samu nasaran gudanar da aikin hajji cikin kwanciyar hankali. Anashi bangaren Jami in tsare tsaren aikin hajjin karamar hukumar Madagali Alhaji Suleiman Yusuf ya shawarci maniyata da

Kamfanin Dangote zaici gaba da taimakawa harkar ilimi a Najeriya.

Image
An kirayi iyaye da su baiwa ilimin yayan su muhimmanci. Babban manajan sashin aiyukan kamfanin dangote dake numan, Alhaji Bello Dan-musa ne yayi wannan kira yayin bukin ranan yara na bana, wanda ya wakana a sashin firamaren makarantan ma'aikatan dangote dake harabar kamfanin a Numan. Babban manajan sashin aiyukan kamfanin dangote, Alhaji Bello Dan- musa yace nasaran karatun duk wani da na da alaka da kokarin iyayen shi. Dan-mua yace Kamfanin dangote zai ci gaba da tallafawa ci gaban ilimi a matakin jaha da na kasa baki daya. Ya kara da cewa kamfanin zai ci gaba da kula da jin dadin malaman makarantan shi kamar yadda ya dace. Shugaban kungiyar malamai da iyaye da malaman makarantan wato PTA, mallam Lawan Adamu yace ware rana na musaman domin bikin ranar yara na da muhimma so sai har ma wa iyaye wadanda ke tallafa wa yaran a kulla yaumin. A cewar shi, koyawa yara sana'oin hannu zai taimaka musu bayan sun manyanta. A nata jawa, shugaban malaman makarantar, misis Grac

Rudunan yan sanda a jahar Adamawa tasha alwashin ceto mutanen da wasu sukayi garkuwa da su a jahar.

Image
Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta baza komarta domin ceto tare da zaukulo wadanda sukayi garkuwa da rev.Mike Ochigbo da pastor John Moses a fadin jahar baki daya. Rundunan ta baiyana hakane a wata sanarwa da ta fitar ta hanun kakakinta SP Suleiman Yahay Nguroje wanda kuma aka rabawa manema labarai a yola. Sanarwan tace dagajin labarin cewa anyi garkuwa da mutanen biyu sai kwamishinan yan sandan jahar ta Adamawa Afolabi Babatola ya bada umurnin tura jami an tsaro domin shiga sako sako dama lunguna domin ganin an kama wadanda sukayi garkuwa da mutanen biyu harma da duk wanda yake da hanu ayin garkuwa da mutanen biyu. Sanarwa ta kuma kara da cewa kwamishin ya umurci dukkanin manyan jami an yan sandan dake fadin jahar da su dukufa wajen sanya ido domin ganin an samu nasaran cika hanu da wadanda sukayi garkuwa da mutanen. Kwamishin ya kuma tabbatarwa da cewa rundunan a shirye take ta kare rayuka da dukiyoyin al umma saboda haka rundunan na bukatan hadin kai da goyon baya daga

Gidauniyar dake yaki da cutar yoyon fitsari a Najeriya ta kudiri aniya kawar da cutar.

Image
An baiyana cewa tsawon nakuda na daya daga cikin abunda ke haddasa cutar yoyon fitsari wanda hakan na jefa uwa da jarirai cikin mawuyacin hali. Shugaban gidauniya fistula a Najeriya Mallam Musa Isa ne ya baiyana haka a lokacinda yake jawabi danhane da ranar yaki da cutar ta yoyon fitsari ta duniya. Mallam Musa Isa yace matsalar samun jinkiri zuwa asibiti da kuma rashin wadatattun cibiyoyin kiwon lafiya musammanma a yankunan karkara suna taimakawa wajen haifar da cutar ta yoyon fitsari. Mallam Isa ya kara da cewa yanayin na talauci da karancin ilimi suma suna taka mahimmiyar rawa wajen musabbabin kamuwa da cutar don haka nema yake kira ga al umma musammanma magidanta da sukasance masu tallafawa matansu a koda yaushe musammanma wadanda ke dauke da juna biyu wanda acewarsa hakan zai taimaka wajen kaucewa kamuwa da cutar ta yoyon fitsari. Harwayau gidauniyar ta fistula a Najeriya ta gabatar da kautukan yabo ga manyan likitoci da suka taka rawan gani wajen yaki da cutar ta

An kirayi maniyata da sukasance masu taka tsantsan da kuma bin doka a lokacin aikin hajji. Suleiman Yusuf.

Image
An kirayi maniyata dake jahar Adamawa da sukasance masu bin dokoki kasar sudiya musammanma a lokacin aikin hajji wanda za a gudanar a wannan shekara domin ganin sun gudanar da aikin hajji karnabbe. Jami in tsare tsaren aikin hajji karamar hukumar Madagali dake jahar Adamawa Alhaji Suleiman Yusuf ne yayi wannan kira a zantawarsa da jaridar All Nur a yola. Alhaji Suleiman yace ya kamata kowane maniyaci ya kasance maibin dukkanin ka idodin aikin hajji da kuma dokar kasa mai tsarki wanda acewarsa hakan zaisa maniyaci yayi aikin hajji karbabbe. Ya kuma shawarci maniyatan da sukasance masu yin taka tsantsan wajen kula da kayakinsu dama jakkunansu domin acewarsa idan sukayi sakaci da jakkunansu wasu zasuyi anfani da wannan damar wajen cutar da su ta sanyamusu wasu kayaki da basu daceba. Don haka nema yace kada maniyaci ya bari wani yazo ya bashi ajiyar kayakin da bai sansuba ko yace rikemini wannan ina zuwa ko sako don ta haka wani yana iya basu kayakin da hwamnatin Saudiya ba

Rundunan yan sandan jahar Adamawa tayi Babban kamu.

Image
Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta kama wasu mutane biyu wadanda suna ciki wadanda suka gudu daga gidan gyara halinka dake Kuje a Abuja. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar wanda kuma aka ranawa manema labarai a yola. Mutanen dai sune Atiku Ibrahim mai shakaru talatin da bakwai da haifuwa sai Adamu Ibrahim mai shekaru Arba in da haifuwa wadanda sun gudu daga gidan gyara halinkan ne biyo bayan hari da aka kai a gidan yarin na kuje a Raman 5-6-22. Wanda yayi sanadiyar mazauna gidan yarin akalla dari biyar suka gudu. Kuma ana tsare da sune bisa zarginsu da satan shanu dama sauran lafuka Wanda kuma suna zaune a gidan yarin ne tundaga shekara ta 2021.biyo bayan zarginsu da safaran makamai kuma su tabbatarwa rundunan jahar Adamawa cewa suna cikin wadanda suka gudu daga gidan yarin kuje. Kuma sun baiyana cewa sunama zaman jiran shariya ne a gidan yarin bisa zarginsu da safaran makamai. Kawo

Sabon kwamandan Civil Defenve a jahar Adamawa ya fara aiki.

Image
Sabon kwamandan Rundunan tsaron bada kariya ga farin kaya.wato Civil defence a Najeriya shiyar jahar Adamawa ya karbi ragamar mulkin rundunan a jahar Adamawa. Jami in watsa labarain rundunan a jahar Adamawa SC Dimas Yakubu Bille ya baiyana haka a wata sanarwa da ya fitar a yola wanda aka rabawa manema labarai. Sanarwan tayi nuna cewa kwamandan rundunan mai barin gado Muhammed Sanusi Bello ya mikawa Sabon kwamandan Ibrahim Mainasara ragamar mulkin rundunan a shelkwatar rundunan dake sakatariyar tarayya dake nan yola. Da yake jawabi kwamanda maibarin gado ya kirayi Jami an rundunan da sukasance masu baiwa Sabon kwamandan hadin kai da goyon baya a koda yaushe domin ganin an samu inganci tsaro a fadin jaha baki daya.ya kuma yabawa Jami an bisa jajircewarsu na ganin an samar da zaman lafiya a fadin jahar. Shima a jawabisa sabon kwamandan Ibrahim Mainasara yayi Alkawarin yin aiki kafada da kafada da Jami an rundunan domin samun cigaba da ma wanzar da zaman lafiya a tsakanin al

Rundunan yan sanda. a jahar Adamawa ta kama magidanci da matarsa bisa zarginsu da cin zarafin maraya.

Rundunan yan sandan jahar Adamawa tana tsare da wani magidanci da matarsa bisa zarginsu da cin zarafin wani maraya dan shekaru sha Daya da haifuwa Mai suna Fahad Abdulkarim Wanda yake karkashin kulawarsu bayan mutuwar mahaifinsa. Kakakin rundunan yan sandan jahar ta Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar a yola Kuma aka rabawa manema labarai a yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Sanarwa tace magidanci Kamal Idris dan shekaru ashirin da hudu da haifuwa da matarsa Ambasiya Idris yar shekaru sha tara da haifuwa dukkaninsu suna zaune ne a cikin anguwar Wuro Jabbe a cikin karamar hukumar yola ta kudu dake jahar Adamawa. Wadanda ake zarginsu da cin zarafin maraya ta raunatashi. Rundunan ta samu rahoton sirrine Wanda Kuma hakan yasa rundunan batayi da wasaba wajen daukan mataki Wanda a yanzu hakama yaron Yana asibiti inda yake jinya. Kwamishinan Yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola ya tabbatar da cewa dazaran an kammala bincike kan w

Rundunan soji na operation hadin kai ta ceto yaran matan chibok biyu daga dajin sambisa a jahar Borno.

Rundunan operation Hadin kai a jahar Borno ta ceto yaran mata biyu yan chibok ciki harda wanda ta haifu kwanan nan gwamnatin jahar zata mikasu ga iyalensu bayan an duba lafiyarsu. Da yake gabatarwa manema labarai yaran mata a shelkwatan rundunan operation Hadin kai a jahar Borno major janar Ibrahim Ali yece a ranan 21-4-2023 ne suka ceto yaran daga dajin Sambisa a jahar ta Borno. Yaran mata biyun dai sun hada da Esther Marcus yar shekaru 26 da haifuwa sai Hauwa Maltha itama yar shekaru 26 da haifuwa. A cewar Hauwa Maltha an cetota tana dauke da cikin wata takwas da sati biyu kuma ta haifi da na miji a ran 28-4-2023 a asibitin rundunan sojojin na bakwai. Rundunan ta baiyana cewa Hauwa Maltha ta auri yan boko haram daban daban har uku kuma dukkaninsu sun gamu da ajalinsu biyo bayan tafo mugama da sukayi da sojiji a tafkin chadi da kuma dajin Sambisa. Ita kuwa Esther Marcus tilastata akayi ta auri mayakin na boko haram wanda aka sani da suna Garus wanda shima an kasheshi

An yabawa yan jarida dangane da yadda suke gudanar da aiyukansu. Alhaji Adamu.

Image
A yayinda aka gufanar da kinin ranan yancin yan jarida ta duniya an yabawa yan jarida bisa jajircewa da sukeyi a duk lokacinda suke gudanar da aiyukansu. Alhaji Adamu Jngi wanda aka fi sani da mai hangene yayi wannan kira a zantawarsa da jaridar Al Nur a yola. Alhaji Adamu Jingi yace yan jarida suna taka muhimmiyar rawa wajen wanzar da zaman lafiya a tsakanin al umma. da kuma ilimantar da al umma baki daya. Alhaji Adamu yace yan jarida suna nan tamkar tsanine a tsakanin shuwagabanin da takakawa don haka ya zama waji a jinjinawa yan jarida. Saboda haka nema ya shawarci al umma da sukasance masu baiwa yan jarida hadin kai da goyon baya domin ganin yan jaridan sun samu damar gudanar da aiyukansu. Alhaji Adamu ya kuma kirayi yan jaridar da sukasance masu gudanar da aiyukansu bil hakki da gaskiya da kuma bin ka idodin aikin jaridan kamar yadda doka ya tanada. Domin samun cigaban aiyukansu yadda ya kamata. Raman uku ga watan mayu na kowace shekarane dai majalisar dinkin d

Matasa da mata sama da dubu hudu ne zasu amfana da shirin koyon sana o i daban daban a jahar Adamawa.

Image
An kirayi matasa dama mata dake fadin jahar Adamawa da su maida hankali wajen koyon sanana o i da zasu dogra da Kansu domin ganin sun kare martabansu dama cigaban all umma baki daya. Shugabar hukumar rage radadin talauci da samar da aikinyi na jahar Adamawa wato PAWECA Hajiya Aishatu Bawa Bello ce tayi wannan kira a jin kadan da duba yadda ake horas da matasa da mata kan sana o i daban daban a jahar Adamawa. Hajiya Aishatu Bawa tace gwamna Ahmadu Umaru Fintiri yana iya kokarinsa na ganin cewa matasa da mata dake fadin jahar sun samu sana o in dogaro da kai Wanda avewarta hakan zai taimaka wajen samar da zamam lafiya dama bunkasa tattalin Arzikin jahar dama kasa baki daya. Hajiya Aishatu tace ada ana biyansu lawus nasu akan dubu biyar to Amman gwamna ya kara musu zuwa dubu goma a kowane watan don haka nema ya shawarci matasan da su maida hankali sosai wajen koyon sana o i. Shima a jawabinsa Kwamishinan ma aikatan koyar da sana o i da samar da aikinyi a jahar Adamawa Mr James Il

Mazauna yankin geriyo sun bukaci da gwamnati ta taimaka musu.

Image
Mazauna yankin geriyo sun kirayi hwamnatin tarayya dana jahar harma dana kananan hukumomi da su taimaka musu da makaranta, da cibiyar kiwon lafiya a yankin domin yaransu su samu inganceccen ilimi. A hiransa da jaridar Al nur Malam Muhammed Na taala Ibrahim Wanda kuma shinema farkon zama a yankin yace sun kwashe akalla shekaru saba in suna zaune ba tare da makaranta ko wata cibiyar kiwon lafiyaba. Don haknema ya zama wajibi su kirayi gwamnatin tarayya dana jahar dana kananan hukumomi harm da kungiyoyi masu zamnan Kansu da su taimaka musu domin ganin yaransu sun samu ilimi yadda ya kamata. Mazuna yankin na geriyo dai akasarinsu masuntane kuma suna zaune ne a daf da bakin tafkin geriyo dake unguwar jambutu a cikin karamar hukumar yola ta arewa fadar gwamnatin jahar Adamawa.

Manoma a jahar Adamawa sunkirayi gwamnatin tarayya da ta taimak musu da inganceccen iri.

Image
Manoma ajahar Adamawa sun kirayi gwamnatin tarayya dana jahar da su taimaka musu da inganceccen iri dama takin zamani domin bunksa harkokin noma harma da samar da wadaceccen abinci a jaha dama kasa baki daya. A hiransu da jarida All nur manoman sukace samarwa manomi inganceccen iri yana da da mutukam muhimmanci ga manomi Wanda hakan zai taimaka wajen Samar amfanin gona mai yawa. Alhaji Muhammed Saleh Gwalan shugaban kungiyar manoma auduga a jahar Adamawa yace dukkanin harkokin noma da manoma zasuyi in basu samu inganceccen iriba to zasu fuskanci matsala a harkokinsu na noma don haka ya zama wajibi su mika kokok baransu ga gwamnatin taryya dana jahar da su agaza musu da wadadattun kayakin noma Wanda hakan zai basu kwarin gwiwar bunkasa harkokin noma a fadin jahar baki daya. Sale gwalan ya kuma kirayi manoma da sukasance masu neman ilimin harkokin noma duba da yanzu harkokin noman na kokarin komawa na zani wato a kimiyance. Saboda haka manoma su tashi tsaye wajen neman sanin yadda

An kirayi gwamnatii jahar Adamawa da ta aiwatar da albashi mafi karanci ga ma aikatan kananan hukumomi N L C

Image
An kirayi gwamnatin jahar Adamawa da ta taimaka wajen magance matsalolin daban daban da ma aikatan jahar ke fama dasu a fadin jahar baki daya. Shugaban kungiyar hadakar kwadigo a Najeriya N L C shiyar Jahar Adamawa Kwamuret Emanuel Fashe ne yayi wannan kira a lokacinda yake jawabi a wurin bikin ranan ma aikata na duniya da aka gudanar a dandalin mahmudu ribadau a yola. Kwamuret Emanuel Fashe yace ma aikatan jahar Adamawa na fuskantar matsaloli da dama da suka hada da aiwata da albashin mafi karanci ga ma aikatan kananan hukumomi, da biyan kudin hutu da ma aikatan kebin gwamnati na shekaru 2017, 2018,2019,2020,2021. da inganta fansho na ma aikatan kananan hukumomi, da kuma sanya hanu kan kudirin doka kan ma aikatan kafafen yada labarain jahar ta Adamawa da dai sauransu. Emanuel Fashe ya kuma kirayi gwamna Ahmadu Umaru Fintiri ya debi malamai a makarantu firamare dake kananan hukumomi aahirin da daya dake fadin jahar duba da karancin malamai da aka fama dashi a makarantun. Har