Posts

Showing posts from August, 2024

Bunkasa Noma: mata hamsin sun samu tallafi kan noma daga kamfanin Dangote a jahar Adamawa.

Image
Kamfanin Dangote dake Numan ta kaddamar da shirin tallafin Naira miliyan biyu da rabi wa mata manoma da dake Ć™auyukan da ke kewaye da ita. A jawabin shi yayin bukin kaddamar wan da ya wakana a harabar kamfanin, gwamnan jahar Adamawa  Umaru Fintiri ya gode wa kamfanin da yadda ya  yunkura domin saka mata cikin shirye shiryen ya na bada tallafi. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri wanda ya samu wakilcin Komishiniyar Ma'aikatar harkokin mata  Neido Geoffrey Kofulto yace mata suna da jajircewa da sa kai a dukkan abun da aka saka su, shi yasa kamfanin Dangote ya ba su wannan dama domin tallafa musu.   Gwamnan ya shawarci matan da suyi amfani da wannan kudin ta hanyar da aka tsara su saboda a samu sakamakon da zai kara bude kofa domin wasu Ć™arin matan su ma su amfana. Fintiri ya godewa sarakunan gargajiyan yankin da yadda suke baiwa Kamfanin goyon bayan tafiyar da ayyukan ta da ma sauran shirye shirye wa mutanen su. A nashi jawabi, daya daga cikin manyan jagororin kamfanin Dangote dake Numan, Ch

Kungiyar Fityanu shiyar karamar hukumar yola ta arewa ta kammala horon da tayiwa Yan agajinta.

Image
  Kungiyar Fityanu shiyar karamar hukumar yola ta arewa ta gudanar da bikin kammala horo da tayiwa Yan agajinta na watanni shida domin karfafa aiyukansu wajen taimakawa Al umma. A jawabinsa a wajen taron Modibbo Safiyanu Iya Runde wakilain malamai jahar Adamawa Wanda Malam Hayatu iya ya wakilta ya baiyana Jin dadinsa tare da cewa aikin agaji abune da yake da mutukan muhimmanci don haka Yan agajin sukasance masu taimakawa jamma a domin kaucewa shiga matsala. Modibbo Safiyanu ya Kuma kirayi Al umma musulmai da sukasance masu Neman ilimin addini da na zamani a Koda yaushe domin acewarsa ilimi shine ginshikin duk abinda zai kawo cigaba dama zaman lafiya  da dai sauransu. Ya Kuma shawarci wadanda aka horar din da suyi amfani da abinda aka koya musu domin ganin an samu cigaban aiyukansu da ma jinkai a tsakanin Al umma baki Daya. Shima da yake nashi jawabi darektan Yan Agajin Fityanu a jahar Adamawa Mallam Sa idu Modibbo Buba ya baiyana cewa an shirya horon ne domin akarawa Yan agajin kwarin

Gwamnatin jahar Jigawa ta aiyana ranan talata a matsayin hutu domin bada damar gudanar da bikin cika shekaru 33 da kirkiro jahar.

Image
  Gwamnatin jahar Jigawa ta aiyana ranan talata 27-8-2024 da ya zama ranan hutu ga ma aikata jahar domin gudanar da bikin cika jahar shekaru 33 da uku da kikiro jahar ta Jigawa. Hakan na kunshene a cikin wata sanarwa daga Jami in yada labarain ofishin shugaban ma aikatan jahar  Isma Ibrahim Dutse ya fitar a jahar. A sanarwar an jiyo shugaban ma aikatan jahar Alhaji Muhammed K Dagaceri na Kiran Al ummar jahar suyi amfani da wannan lokacin wajen yiwa jahar ta Jigawa dama kasa adu o I domin Samar da zaman lafiya dama cigaba. Sanarwan ta Kuma baiyana cewa dafatan dukkanin ma aikatan jahar zasu Yi amfani da ranan wajen godewa Allah madaukakin sarki taro da adu ar Allah ya kawo zaman lafiya hadin Kai dama cigaba a jahar Jigawa. Ya Kuma kirayi jama a da su yiwa wadanda ambaliyar ruwa ya shafa a wasu sassan jahar Adu a,  lamarin da yayi sanadiyar rasa rayuka dukiyoyyi masu yawa. A shekara ta 1991 ne dai aka kirkiro jahar Jigawa karkashin mulkin soja Gen. Ibrahim Badamasi Babangida.

Yan sanda biyu sun gamu da ajalisu tare da jikkata uku a wani hari da aka Kai akan Jami an Yan sanda a Abuja.

Image
  Jami an Yan sanda biyu ne suka rasa rayukansu a yayinda uku suna cikin wani yanayi na jikkata tare da cinnawa motoci Yan sandan wuta, sakamokon hari da ake zargin mabiya darikar shiya ne suka kaiwa Yan sanda a dai dai lokacinda suke gudanar da aiyukansu a shingen binciken ababen hawa dake mahadar wusai a birnin tarayya Abuja. Kakakin rundunan. Yan sandan Abuja SP Josephine Adeh ta baiyana haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a madadin kwamishinan Yan sandan na Abuja. Kwamishinan Yan sandan Abuja Benneth C Igweh yayi Allah wadai da wannan hari na rashin tausayi da aka kaiwa Yan sanda tare da yin alkawarin hukunta duk Wanda aka samu da laifin akata haka inda yace kawo yanzu komai Yana tafiya dai dai a inda lamarin ya faru.

Sarkin Ningi ya rasu Yana da shekaru 87.

Image
 Rahotanni daga jahar Bauchi na cewa Allah yayiwa Sarkin Ningi Alhaji Yunusa Muhammed Danyaya tasuwa. Basaraken ya rasune a wani asibiti dake Kano bayan kwanaki biyu da ya dawo daga duba lafiyarsa a kasar Saudiya. Kuma ya rasu Yana da shekaru 87 da haifuwa. Hakan na kunshene a cikin wata sanarwa daga sakataren fadar Alhaji Usman Sule magayaki Ningi. Tare da baiyana cewa za ayi jana izarsa da misalin karfe 4:00 na yamma a fadarsa dake Ningi.A Ladin nan 25-82024.

Sabon kwamandan Rundunan tsaro na Civil Defence a jahar Adamawa ya kama aiki.

Image
  Rundunan tsaro bada kariya ga fararen hula wato Civil Defence shiyar jahar Adamawa ta marabci  sabon kwamandan ta Idris D Bande Wanda tuninma ya fara aiki a hukumance Jin kadan da karabar ragamar shugabancin rundunan daga Wanda ya gada Ibrahim Mainasara. An dai bikin marabtar sabon kwamandan ne a shelkwatar rundunan ta NSCDC dake nan Yola. Kakakin rundunan. ta NSCDC a jahar Adamawa DSC Nyako Amidu Baba ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola. Fadar gwamnatin jahar Adamawa. Sabon kwamandan dai an sauya masa wurin aiki ne daga yankin B dake jahar Kaduna Wanda ya maye gurbin Ibrahim Mainasara Wanda yayi aiki na tsawon shekara Daya da watanni uku Kuma shine kwamandan rundunan na 15 a jahar Adamawa. A lokacinda yake mika ragabab shugabancin rundunan ga sabon kwamandan Ibrahim Mainasara ya kirayi dukkanin Jami an rundunan da su baiwa sabon kwamandan cikekken hadin Kai da goyon baya domin tabbatar da ganin cewa rundunan ta cigaba da gudanar da aiyukan da suka d

PCRC dake Jambutu sun junjinawa rundunan yan sandan jahar Adamawa.

Image
  Al umma dake taimakawa rundunan Yan sanda wato PCRC shiyar anguwar Jambutu ta yabawa rundunan Yan sandan jahar Adamawa  bisa kokarinta na inganta tsaro a lokacin zanga zangan kasa da ya gudana a fadin Najeriyar. Shugaban PCRC dake Jambutu Alhaji Adamu Jingi Wanda akafi sani da Mai hange ne ya yi wannan yabo a zantawarsa da manema labarai a Yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Alhaji Adamu Jingi yace rundunan yan sandan ta taka rawan ganin wajen inganta tsaro a lokacin zanga zangan a jahar Adamawa saboda haka rundunan ta cancanci yabo saboda irin wannan na mijin kokari da rundunan Yan sandan tayi. Alhaji Adamu ya Kuma baiyana cewa  yabon Gwani ya zama dole domin rundunan yan sandan karkashin jagoranci kwamishinan Yan sandan jahar Adamawa Dankwambo Morris tayi kokari wajen kare rayuka dama dukiyoyin Al umma a fadin jahar Adamawa. Adamu Jingi ya Kara da cewa PCRC dake shiyar Anguwar Jambutu a shirye take ta baiwa rundunan Yan sandan hadin Kai da goyon baya domin ganin ta samu nasaran kar

FOMWAN shiyar Jahar Adamawa ta yabawa gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jahar Adamawa.

Image
Kungiyar mata musulmai ta tarayya FOMWAN shiyar jahar Adamawa.  tana Mai godewa Mai girma gwamnan jahar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri da mataimakiyarsa Farfesa Kaletapwa Farauta bisa na mijin kokari da suke Yi na tallafawa mata dangane da sana o I a fadin jahar Adamawa. Hajiya Khadija Buba Wanda Kuma itace amiran Kungiyar ta FOMWAN a jahar Adamawa ta baiyana haka a lokacinda take zantawa da manema labarai a Yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Hajiya Khadija tace gwamna Fintiri ya taka rawan ganin wajen taimakawa mata musammanma a bangaren Samar musu da sana o I dogaro da Kai Wanda Kuma hakan zaitaimaka wajen rufawa kansu asiri. A cewarta dai gwamnan ya basu takardun da za acike domin taimakawa matan har kuda Dari inda hakan ya basu damar rarrabawa a rassansu na kananan hukumomi ashirin da daya dake fadin jahar Adamawa. To a gaskiya ba abida za mucewa gwamna Fintiri sai godiya tare da Yi masa fatan Allah ma daukakin sarki ya bashi damar cigaba da aiyukan cigaban jahar Adamawa baki Daya.

PCRC ta yabawa rundunan Yan sandan jahar Adamawa.

Image
  Al umma dake taimakawa Yan sanda wato PCRC shiyar jahar Adamawa sun yabawa rundunan Yan sandan jahar Adamawa bisa nuna kwarewarsu a lokacinda aka gudanar da zanga zangan kasa. Kakakin rundunan yan sanda a jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola. Shugaban Al umma dake taimakawa rundunan Yan sanda Hon. Musa Bubakari Kamale da yake mikawa kwamishin Yan sandan na jahar Adamawa Dankwambo Morris takardan yabon a shelkwatan rundunan yan sandan dake Yola, ya baiyana cewa rundunan tayi abin Azo a yaba saboda haka ya zama wajibi a yabawa rundunan bisa na mijin kokari da sukayi na inganta tsaro da Kuma nuna kwarewarsu wajen kula da yadda aka gudanar da zanga zanga. PCRC sun Kuma jinjinawa rundunan bisa kokarinta na wanzar tare da tabbatar da zaman lafiya da Kuma ganin an kammala zanga zangan ba tare da matsalaba. Da yake karban takardan yabon Kwamishinan Yan sanda Dankwambo Morris ya yaba da irin wannan karramawa da PCRC suk

Shugaban kasa Bola Tinubu ya nada sabon shugaban hukumar Aikin hajji ta kasa. NAHCON.

Image
  Shugaban kasan Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da nada Farfesa Abdullahi Sale Usman a matsayin shugaban hukumar Aikin Hajji ta kasa wato NAHCON. Mashawarci  na musamman kan harkan yada labarai ga shugaban kasa Ajuri Ngelale ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitara a litinin din nan. Nada sabon shugaban na zuwa ne bayan sallama shugaban Hukumar ta NAHCON Malam Jalal Arabi Wanda shugaban kasar ya sallama biyona zarginsa da almudahana da kudin da yaki nera bilyon 90 Wanda gwamnatin tarayya ta baiwa hukumar a matsayin tallafi ga aikin hajjin shekara ta 2024. An sallami Jalal daga kan mikamin shugabancin hukumar aikin hajji ta kasan ne bayan kwanaki hudu da hukumar dake yaki da cinhanci da rashawa wato EFCC  ta kamashi bisa tukumarsa da yin na daidaiba da kudaden hukumar. Shugaban kasa yace Yana Mai tsammanin sabon shugaban zai gudanar da aiyukansu yadda ya kamata domin inganta hukumar.

Hukumar raya yankin Arewa Masau gabas NEDC zata fara aikin gyaran gadar Waga kamar yadda shugaban kasa ya bada umurnin.

Image
Shugaban kasa  Bola Ahmed  Tinubu ya amince da a gaggauta ginin gadan yankin Wagga na Karamar hukumar Madagali wanda ruwa ya cinye.  Babban manajan hukumar ci gaban yankin arewa maso gabas NEDC ,  Mohammed Alkali Goni  ne ya fadi haka yayin hirar shi da manema labaru jim kaÉ—an bayan duba gadan a Madagali . Mohammed Alkali Goni yace bayan da shugaban kasa Bola   Ahmed  Tinibu ya samu labarin  wannan ibtila'a, ya amince wa hukumar ci gaban yankin arewa maso gabas da ta gaggauta fara aikin ginin gadan domin kiyaye karin munin yanayin a yankin.   Alkali Goni yayi bayanin cewa lamarin akwai tada hankali matuka ganin ya shafi yadda al'umma ke fita neman halaliyar su  shi yasa shugaban kasa ya gaggauta amincewa da aikin gadar domin kiyaye aukuwar haka nan gaba.  A cewar babban manajan, tawagar hukumar da masu aikin kwangilar sun iso ne domin gane wa ido , sannan su bullo da dabarbarun da za su taimakawa al'umma nan take, kan a fara aikin ginin gaÉ—ar. Har wa yau tawagar hukumar da

Kungiyoyin NACOMYO Dana YOWICAN sun shirya taron kan zaman lafiya a jahar Adamawa.

Image
An shawarci Al umma Musulmai da mabiya addinin kirista da sukasance masu hada kansu domin wanzar da zaman lafiya  dama daurewan cigaba a jahar Adamawa dama kasa baki Daya. Mt Morris Vonovalki ne ya bada wannan shawara a lokacin da yake jawabi a wurin taron wanzar da zaman da zaman lafiya Wanda kungiyar matasa Musulmai NACOMYO da na matasa kirista YOWICAN suka shirya a Yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Morris yace yanzu lokaci yayi da ya kamata a maida hankali wajen Samar da hadin Kai da Kuma kaucewa banbance banbancen addini Dama kabilanci a hadu a Gina kasa domin samu dauwamammen zaman lafiya. Ya Kuma yabawa kungiyoyin NACOMYO da YOWICAN bisa shirya wannan taro tare da fatan taron zai zama silar Samar da hadin Kai a tsakanin mabiya addinain biyu. Anasu jawabai shugaban majalisar addinin musulunci a jahar Adamawa Mallam Gambo Jika da shugaban kungiyar CAN a jahar Adamawa Rev Joel Manzo dukkaninsu sun nuna farin cikinsu da Jin dadinsa dangane da shirya wannan taro tare da Kiran kungiy

Gidauniyar Attarahum tayi feshin Magani Sauro a Anguwannin Runde da Doubeli.

Image
  Gidauniyar Attarahum ta kaddamar da fara feshin Magani sauro a anguwannin Runde da Doubeli a wani mataki na yaki da zazzabin cizon sauro a tsakanin Al umma. Feshin dai ya gudanar ne karkashin shugaban kungiyar a karamar hukumar yola ta Arewa fadar gwamnatin jahar Adamawa Mallam Abubakar Abdullahi Isa. Da yake zantawa da manema labarai a yayin feshin shugaban Gidauniyar a karamar hukumar yola ta Arewa Mallam Abubakar Abdullahi Isa yace dalilinsu na kaddamar da feshin shine Yana Daya daga cikin aiyukansu na tallafawa Al umma domin acewarsa gidauniyar tana hanyoyin tallafawa Al umma da yawan gaske saboda haka yasa suka ga ya dace su gudanar da feshin duba da yadda ake cikin damina Wanda Kuma ake samu yawaitar sauro a tsakanin Al umma. Yace Yana daga cikin aiyukan gidauniyar na tallafawa marayu, marassa galihu, matan da mazajensu suka rasu Kuma suka barsu da yara, harma suna taimakawa a bangaren karatu da dai sauransu. Ya Kuma  kirayi daukacin Al umma jahar Adamawa da sukasance masu tsaf

Kungiyoyin NACOMYO Dana YOWICAN sun kaddamar da dashen itatuwa a jahar Adamawa.

Image
 A wani mataki na wanzar da zaman lafiya a da hadin Kai a tsakanin Al umma kungiyoyin matasa musulmai wato NACOMYO Dana matasa mabiya addinin kirista YOWICAN sun gudanar da gangamin dashen itatuwa Wanda aka kaddamar a makarantar old G R A dake unguwar NEPA a jahar Adamawa. Kungiyoyin biyu dai suke sun dauki matakin haka ne domin Samar da zaman lafiya dama hadin Kai a tsakanin Al umma a wani matakin na cigaban jahar Adamawa dama kasa baki Daya. Da yake jawabi Ko odinata kungiyar NACOMYO a jahar Adamawa Mallam Abdullahi ibn Hamman yace dashen itatuwa abune dake da mutakar muhimmanci don haka akwai bukatar a maida hankali wajen dashen itatuwa domin Samar da zaman lafiya dama hadin Kai a tsakanin Al umma. Abdullahi Hamman ya jadda aniyar kungiyoyin na gudanar da aiyukan da zai Samar da hadin Kai da zaman lafiya mai daurewa a tsakanin Al umma. Ya Kuma baiyana cewa zasu fadada wannan dashen itatuwa har zuwa ga daukacin kananan hukumomi 21 dake fadin jahar Adamawa Wanda acewarsa hakan zai Sam

Rundunan Yan sandan jahar Adamawa ta umurci Jami anta da su tabbatar abi dokan hana Bola Bola a fadin jahar.

Image
  Rundunan Yan sandan jahar Adamawa ta murcin manyan Jami anta dake ofisoshinta a fadin jahar Adamawa da su tabbatar abi dokan nan da gwamna Ahmadu Umaru Fintiri ya sanyawa hanu na haramta aiyukan bala bala a fadin jahar. Kamishinan Yan sandan jahar Adamawa Dankwambo Morris ne ya baiyana haka a wata sanarwa daga kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ya rabawa manema labarai a Yola. Umurnin ya shafi dukkanin kananan hukumomi ashirin da daya dake fadin jahar har zuwa wani lakoci da ba a baiyanaba. Kwamishinan Yan sandan yace duk Wanda aka samu da aiyukan Bola Bola daga ran 15-8-2024 to ya aikata laifi za a kamashi Kuma a gurfanar dashi a gaban kotu. Kawo yanzu dai rundunan ta baza Jami anta domin Saka kafar wando Daya da duk Wanda yayiwa dokan biris, saboda haka dokan zatayi aiki akan Wanda ya yiwa doka Karan tsaye.  Saboda haka rundunan ta gargadi dukkanin masu aikata Bola Bola da su nisanta kansu su baiwa hukumomin tsaro da aka tura domin ganin anbi dokan

Rikici a tsakanin manoma da makiyaya yayi sanadiyar mutuwar mutane uku a jahar Adamawa.

Image
  Kawo yanzu dai kura ta lafa a yankin Kodomun biyo bayan tashin hankali da aka samu a tsakanin manoma da makiyaya a karamar hukumar Demsa dake jahar Adamawa, acewar rundunan yan sandan jahar Adamawa. Rundunan Yan sandan ta baki kakakinta SP Suleiman Yahaya Nguroje yace yanzu kowa na gudanar da harkokinsu yadda ya kamata domin an tura Jami an tsaro a inda lamarin ya faru. SP Suleiman Yahaya Nguroje ya baiyana cewa tunin kwamishinan Yan sanda jahar ya Adamawa Dankwambo Morris ya bada umurnin gudanar da bincike dangane da lamarin. A cewarsa tunin aka kama mutane uku da ake zargi da hanu a rikicin Wanda a yanzu haka ana gudanar da bincike akansu. Tare da Kiran dukkanin masu ruwa da tsaki su taimaka wajen magance matsalar baki Daya. Rikincin dai yayi sanadiyar mutuwar mutane uku tare da asaran dukiyoyi masu yawa. SP Suleiman Yahaya ta Kuma shawarci Al umma da su daina daukan doka a hanu su rinka Kai rahoton dukkanin abinda basu yarda daahiba zuwa ga ofishin hukumomin tsaro.

Jami ar Modibbo ta samu sabon mataimakin shugaban Jami ar.

Image
  Biyo bayan zamanta karo na 17 majalisar zantarwar Jami ar Modibbo Adama dake Yola tayi la akari da amincewa da zaban Farfesa Ibrahim Umar a matsayin mataimakin shugaban Jami ar Modibbo Adama Wanda Kuma shine na tara cikin jerin sunayen mataikan shugabannin Jami ar. Shugaban majalisar zantarwar Kuma pro-chancellor na Jami ar Modibbo Adama dake Yola H. E. Mahmud Aliyu Shinkafi ne ya sanar da haka a kashen taron majalisar  Farfesa Ibrahim Umar. Farfesa ne a tsangayar kare tsirrai Kuma ya fito ne daga karamar hukumar Gombi dake jahar Adamawa. Kuma ya shugabancin kwalenin fasaha ta jahar Adamawa na tsawon shekaru biyar. Shugaban sashin yada labarai Jami ar Modibbo Adama Aminu Julde Gurumpawo ne ya baiyana haka a wata sanarwa da aikewa manema labarai a Yola.

Rundunan Yan sanda jahar Adamawa ta karawa Jami anta 120 Karin girma na mataimakin safritandan.

Image
  Kwamishinan Yan sandan jahar Adamawa Dankwambo Morris ya likawa Jami an Yan sanda Dari da ashirin girma a matsayin mataimaka safritandan Yan sanda. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola. Karin girman ya biyo bayan amincewa da hukumar aiyukan Yan sanda wato PSC tayi dukkanin Jami an Yan sanda 120 da suka samu Karin girma da sifeta zuwa matakin safritandan a jahar Adamawa wato ASP an basu ne bisa kwarewa da cancantansu . Kwamishinan ya taya su murnan samun wannan mukami tare da ahawartansu da suyi amfani da mukamin da suka samu ta hanyar da suka dace da Kuma bin dokokin aiki tare dayin abinda zasu samu yabo daga Al umma, tare da gudanar da adalci a yayin aiyukansu da dai sauransu. Bayan ga tawagan kwamishinan Yan sanda Yan uwa da abokan Arziki sun halar bikin likawa Jami an Yan sandan mikamin Wanda akayi Police officers mess dake nan Yola.

Gwamnan jahar Adamawa ya yabawa rundunan tsaro Civil Defence.

Image
  Rundunan tsaro bada kariya ga fararen hula wato Civil Defence dake jahar Adamawa ta karbi takardan yabo daga gwamnan Ahmadu Umaru Fintiri na jahar Adamawa ta Mai bashi shawara na musamman akan tsaro da zaman lafiya Hon. Ahmed Lawan. Wannan yabon dai na zuwane bayan da rundunan NSCDC  ta taka mahimmiuar rawa wajen inganta tsaro musammanma a lokacin zanga zangan kin jinin gwamnati da akayi na kwanaki goma. Ahmed Lawan yace rundunan batayi da wasaba na ganin an tabbatar da zaman lafiya da Kuma bin doka da oda a fadin jahar. Sama da shekaru da suka shude. Kuma rundunan ta nuna kwarewarta matuka tare da gudanar da aiyukanta tukuru domin kare rayuka dama dukiyoyin Al umma  Zanga zanga da aka gudanar ya haifar da kalubalen tsaro a fadin Najeriya duba da yadda ya yadu zuwa wasu sassa bisa bukatar kyakkawar gwamnati da Kuma adalci amman a jahar Adamawa ba asamu matsalaba saboda irin rawanda rundunan tsaro NSCDC ta taka wajen inganta tsaro. A jawabinsa Kwamandan Rundunan a jahar Adamawa Ibrahi

Gwamnatin jahar Adamawa ta jinjinawa Rundunan Yan sandan jahar Adamawa.

Image
  Gwamnatin jahar Adamawa ta jinjinawa rundunan yan sandan jahar Adamawa bisa kokarinta na inganta tsaro a lokacin zanga zangan kasa da akayi. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola. Sanarwan tace a hunkunce gwamnatin jahar ta Adamawa ta yabawa rundunan yan sandan bisa nuna kwarewarsu  wajen gudanar da aiyukansu na kula da zanga zangan kasa Wanda hakan yasa ba a samu tashin hankaliba. Da yake gabatar da takardan yabo a madadin gwamnatin jahar Adamawa mashawarci na musamman akan harkokin tsaro ga gwamna jahar Adamawa Hon. Ahmed Lawan ya jinjinawa rundunan Yan sanda bisa kokarinsa na maida hankali domin ganin an Samar da zaman lafiya da inganta tsaro kafin, da lokacin harma da bayan zanga zanga. Kwamishinan Yan sandan jahar Adamawa Dankwambo Morris ya baiyana farin cikinsa da godiyarsa ga gwamna Umaru Fintiri  bisa wannan yabo da yayiwa rundunan, ya Kuma godewa Al umma jahar Adamawa bisa h

Makarantar Sabilur Rashad ta cika shekaru 20 da kafuwa.

Image
  Makarantar Sabilur Rashad dake cikin karamar hukumar yola ta kudu tayi bikin cika shekaru 20 da kafuwa Wanda Kuma bikin ya samu halartan Jama a da dama wadanda suka fito daga ciki da wajen jahar Adamawa.   Farfesa Abdullahi Liman Tukur tsahon mataimakin shugaban. Jami ar Modibbo Adama dake nan Yola Wanda Kuma shine Bako Mai jawabi a wurin bikin ya ja hankalin Al umma da sukasance masu maida hankali wajen baiwa yara ilimi kasancewa sune shuwagabanin gobe  Liman Tukur Wanda Dr Abubakar Bello Jada ya wakilta yace Ilimi Yana da mutukan muhimmanci saboda haka kar ayi da wasa wajen baiwa ilimi muhimmanci Wanda acewarsa hakan zai taimaka wajen rage yawan yaran da basu zuwa makarantar. Ya Kuma yabawa makarantar ta Sabilur Rashad bisa na mijin kokari da sukayi na ganin cewa yara sun Sami ingancaccen ilimi saboda haka nema yake kira ga sauran makarantu da suyi koyi da makarantar Sabilur Rashad domin ganin an samu damar bunkasa ilimi a tsakanin yara. Ya yabawa malamai bisa hakuri da juriua da s

An karrama Dr Jauro Jalo .........cibiyar ISANRRC.

Image
  Dr kwamuret Jauro Jalo Wanda Kuma shine Babban rijistiran cibiyar bincike mu adinai da harkokin noma ta kasa wato ISANRRC kenan a takaice ya samu karramawa na musamman daga cibiyar ta ISANRRC na ma tsagi doctor. Babban directan Cibiyar ta ISANRRC na kasa Dr John Daniel Enemoma ya jagoranci baiwa Dr Jauro Jalo karramawa Dokto Wanda ya gudana a Abuja. Da yake magana Dr Jauro Jalo ya godewa Allah madaukakin sarki da yasa aka mashi wannan karramawa tare Kuma da yabawa cibiyar ta ISANRRC da ya bashi wannan matsayi na Dokta. Dr Jauro Jalo ya Kuma godewa Yan uwa da abokan Arziki bisa irin hadin Kai da goyon baya da suka bashi da Kuma Yi mishi adu o I Wanda hakan ya Kai ga bashi wannan dama saboda haka Yana mutukan godiya. Dr Jauro ya shawarci Yan Najeriya da su daina aibanta shuwagabannin kamatayi sukasance masu yiwa shuwagabani adu o I a Koda yaushe Wanda a cewarsa haka zai taimaka wajen cigaban kasa baki Daya. Dr Jalo ya Kuma kirayi Yan Najeriya da su maida hankali wajen baiwa shuwagabani

Majalisar matasa Musulmai a Najeriya NACOMYO ta nisanta kanta daga zanga zanga da akeyi a fadin Najeriya.

Image
 Majalisar matasa musulmai a Najeriya shiyar jahar Adamawa  NACOMYO ta nisanta kansa daga zanga zangan lumana da wasu matasa da ma kungiyoyi suka kudiri aniyar yi a fadin Najeriya. Ko odinetan majalisar a jahar Adamawa Alhaji Abdullahi ibn Hamman ne ya baiyana haka a taron manema labarai da ya gudanar a Yola. Alhaji Abdullahi Hamman yace a matsayin majalisar matasa musulmai basu amince da zanga zanga ba saboda zanga zanga a addinin musulunci jaramunne, saboda  haka basuga dalilin da yasa zasu Sa kansu cikin yin zanga zangan ba. Ibn Hamman yace yin zanga zanga ya saba karantarwan addinin musulunci domin a cikin Al Qur ani Mai girma da hadisi duk sun la anci zanga zanga misalin a cikin Al Qur ani sura ta 5 aya ta 32 da sura ta 2 Aya ta 208 duk suyi hani kan tada husuma saboda haka suna masu Allah wadai da shirya wannan zanga zanga. Ko odinaton yace musulunci Yana karantar da zaman lafiya da Kuma hadin Kai saboda haka majalisar matasa. ta musulmai  wato NACOMYO bata goyon bayan zanga zang

With a Bruised Image, Yet Wafari Theman Eyes the Dougirei House.

Image
By Maliki Salaudeen  Yola Wafari Theman, once a prominent member of the Adamawa State House of Assembly representing a constituency in Hong Local Government, served from 2011 to 2015 under the defunct Action Congress of Nigeria (ACN), which later evolved into the All Progressives Congress (APC). After defecting to the APC, Theman served as the State Secretary in Adamawa prior to the 2023 general election, where he sought the governorship but finished last among his party's aspirants. Since then, Theman has been entangled in controversies involving unfulfilled promises made during contributions in his local church and community associations. This pattern has made him a burden at social functions, leading to his diminishing presence and eventual removal as the APC Secretary and a poor performance in the 2023 party primaries. In a bid to revive his political career, Theman joined the Social Democratic Party (SDP) as its Vice Chairman in the North East late last year. However, his past

Senator Girei Calls on Protester to Give Government more time and Urges them to Suspension of protest.

Image
  By Ibrahim Abubakar Yola. Abuja, Nigeria – Senator Abubakar Halilu Girei has called on #Endbadgovernance protesters to suspend their nationwide demonstrations and give the federal government until the end of the year to address their concerns. In a statement released on Thursday, the APC chieftain acknowledged that the protests have successfully prompted the government to begin implementing policies that are more responsive to the needs of the people. "The agitation leading up to the protests has awakened the government to its responsibilities, resulting in the implementation of people-friendly policies that are already making a positive impact," Girei said. He highlighted several government actions that have been taken in response to the protests, including tax waivers on imported food items, addressing the minimum wage issue, signing the minimum wage act into law, providing incentives to farmers, and offering various palliatives. "The latest stance by Civil Society O

Greening Taraba: Taraba Govt, military partner to mitigate effects of climate change

Image
  By Sani Yarima  Jalingo. The Taraba State Commissioner of Environment and Climate Change, Aisha Barde, has emphasized the state government's dedication to improving ecological balance, conserving biodiversity, and restoring degraded lands as part of broader climate action for mitigation measures.  She made this commitment during the tree-planting event, held in collaboration with the Nigerian Army at the permanent site of the 6 Brigade Jalingo, the state capital on Saturday, 27 July 2024. Barde highlighted that the GREENING TARABA Initiative aims to promote environmental sustainability and combat climate change, as well as create awareness within the State and the North East region of the nation.  She also pointed out that Nigeria, through the Designated National Authority, is committed to reducing greenhouse gas emissions by 20% unconditionally and 47% conditionally with international support between now and 2030 through its Nationally Determined Contributions under the Paris Ag

Gwamnatin jahar Adamawa ta lashi takwabin kare rayuka dama dukiyoyin Al umma................Ahmed Lawan.

Image
  A wani mataki na inganta tsaro da Samar da zaman lafiya harma da cigaban jahar Adamawa an kirayi daukacin mazauna jahar da sukasance masu baiwa gwamnatin gwamna Ahmadu Umaru Fintiri hadin Kai da goyon baya domin ya samu damar gudanar da aiyukan cigaban jahar baki Daya. Mashawarci na musamman akan harkokin tsaro ga gwamna Fintiri na jahar Adamawa Ahmed Lawan ne yayi wannan kira a zantawarsa da manema labarai a Yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Ahmed Lawan yace Al ummar jahar Adamawa su Sani bamu da wata jahar da ta wuce Adamawa Kuma ba mu da wata kasa da ta wuce Najeriya saboda haka mu nisanta kammu daga dukkanin abinda zai kawo wa jaharmu ko kasarmu koma baya. Ahmed ya Kuma baiyana cewa Yana da muhimmanci abaiwa gwamnatin hadin Kai kasancewa gwamnati karkashin jagoranci gwamna Fintiri ta dukufa wajen inganta tsaro ba dare ba rana domin ganin ta tabbatar da kare rayuka dama dukiyoyin Al umma baki Daya. A cewarsa dai jahar Adamawa jaha ce da take na gaba gaba wajen cigaba a fadin Naj

Rundunan tsaron Civil Defence dake jahar Adamawa tace ta kimtsa tsaf domin kare rayuka da dukiyoyin Al umma.

Image
  Rundunan tsaro dake bada kariya ga fararen hula wato Civil Defence a Najeriya shiyar jahar Adamawa tace ta kimtsa tsaf domin bada kariya da Kuma ganin an gudanar da zanga zangan lumana cikin tsanaki na tare da wata matsalaba a fadin jahar Adamawa. Kakakin rundunan a jahar Adamawa DSC Nyako Amidu Baba ne ya baiyana haka a zantawarsa da manema labarai a ofishinsa dake Yola. DSC Amidu yace tuninma suka tura Jami ansu a muhimmain wurarai domin ganin ba ayiwa Al umma barnan kayakinsu saboda sun dauki dukkanin matakai da suka gabata domin ganin an kammala zanga zangan lafiya. Ya Kuma tabbatar da cewa rundunarsu Daman tun daga lokacinta aka fara maganan shirya wannan zanga zanga bata barci da idonta biyu inda ta kudiri aniyar ganin ba a samu tsekoba. DSC Nyako ya tabbatarwa Al ummar jahar Adamawa cewa rundunan a shirye take ta kare rayuka dama dukiyoyin daukacin Al ummar dake fadin jahar domin ganin an samu zaman lafiya mai daurewa a fadin jahar baki Daya. Harwayau ya shawarci jama a da suk

Rundunan yan sandan jahar Adamawa tace ta dauki dukkanin matakai da suka dace domin tinkara zanga zangan lumana

Image
  Rundunan Yan sandan jahar Adamawa ta lashi takwabin ganin ba a samu wata hayaniyaba a lokacin gudanan da zanga zangan lumana da wasu kungiyoyin matasa da suka kitsayi da sunan kawo karshen matsanancin rayuwa da ake fuskanta a fadin Najeriya. Rundunan ta baiyana haka ne ta bakin kakainta SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a zantawarsa da manema labarai a ofishinsa dake Yola. Kakakin rundunan. yace kawo yanzu dukkanin matakai da ya kamata a dauka sun dauka domin ganin zanga zangan ya tafi cikin lumana ba tare da an jikkata kowaba. SP Suleiman tuninma suka kafa shingen binciken ababen hawa a dukkanin mashigan fadar gwamnatin jahar domin ganin an Samar da zaman lafiya a tsakanin Al umma. Nguroje yace Yana daga cikin matakai da suka dauka na tura Jami an su zuwa sako sako domin sanya ido akan dukiyoyin Al umma da Kuma baiwa jama a kariya a duk inda suke a fadin jahar. SP Suleiman Yana Mai tabbatarwa Al ummar jahar ta Adamawa cewa rundunan bata barci da idonta biyu yanayin dukk

Northern Traders Association Appeals To It's Members, Nigerians To Desist From August Protest

Image
Northern Nigeria Traders Association has urged Nigerians, especially the youth and its members to avoid any act capable of destroying the Country. Alhaji Muhammed Ibrahim 86 who is the Chairman Northern Nigeria Traders Association made the call while speaking with Newsmen in Yola, Adamawa state capital.  The call came after some youths planned a Nationwide protest Following the harshness that Nigeria Facing. Alhaji Muhammed Ibrahim said the protest is not a solution our problems are better to consider with prayer to seek Allah to come to an end of hardship for peace and development. Alhaji Ibrahim advised all members of the Northern Nigeria Traders Association to distance themselves from their selves from the protest and avoid breaking the law in the country. Ibrahim stresses that always protests affect the traders directly, so therefore don't commit themselves to the protest. He called on the federal government to do everything possible to create job opportunities for youth throug