Posts

Showing posts from November, 2023

Babban Hafsan tsaron Najeriya ya gana da Babban sifeton yan sandan Najeriya.

Image
A wani mataki na inganta tsaro da kuma hadin gwiwa a tsakanin hukumomin tsaro, Babban Hafsan tsaron Najeriya janaral Christopha Gwabin Musa tare da manyan Jami an soji sun ziyarci Babban sifeton yan sandan Najeriya a ofishinsa dake shelkwatar rundunan a Abuja domin kara karfafa halaka da kuma hada kai wajen yin aiki tare a tsakanin yan sandan da sojoji domin kare kasa daga matsalar tsaro. Kakakin rundunan yan sandan na kasa ACP Olumuyiwa Adejobi ne ya baiyana haka a wata sanarwa da ya fitar wanda kuma aka rabawa manema labarai a Abuja. Babban Hafsan tsaron ya taya Babban sifeton yan sandan murnan tabbatar da nadinsa a matsayin Babban sifeton yan sandan Najeriya tare yaba masa bisa kokarinsa na tura rundunan yan sandan kwantar da tarzoma domin dakile aiyukan masu tada kayan baya. Tare kuma da nuna alhininsa da harin da wasu sojoji suka kai a shelkwatan rundunan yan

Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta taimakawa iyalain Jamin an yan sanda da suka gamu da ajalinsu a bakin aiki.

Image
A kokarinta da kula da walwan Jami an yan sadan rundunan yan sandan a Najeriya ta bigi kirjin cigaba da kula da walwalan Jami an yan sandan a koda yaushe domin kara musu gwiwar gudanar da aiyukansu yadda ya kamata. Rundunan karkashin shirinta na inshora. Kwamishinan yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola ya gabatarwa magadan yan sandan da suka rasa rayukansu a lokacinda suke yiwa kasa aiki. Takardan karban kudi wa iyalen 32 kudin wanda yawansa yakai Milyon 73,357,394,83. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar a Yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Kwamishinan ya kuma jadda da aniyar rundunan nayin dukkanin abinda suka dace domin sauke nauyin da yake kanta na kula da jin dadin dukkanin Jami an yan sandan harma da wadanda suka

Gwamnatin jahar Adamawa ta amince da bada kwangila gyara hanya da ta tashi daga Damare zuwa Barong.

Image
Gwamnan jahar Adamawa ta amince da bada kwangilar aikin hanya mai tsawon kilomita arba'in da biyu, daga sansanin horar da matasa masu yiwa ƙasa hidima zuwa kauyen borong. Komishinan ilimi, Doctor Garba Umar Pella ne ya baiyana haka yayin da yayi wa manema labaru jawabi jim kaɗan bayan kammala zaman majalisar jaha karo na takwas wanda gwamnan jaha ya jagoranta. Doctor Garba Umar Pella yace ganin muhimmancin hanyar wanda ta ratsa tsakanin kananan hukumomin demsa da Girei, gami da irin wahalhalu da mutanen da ke yankin ke sha, gwamnatin jahar taga ya kamata ta bada wannan aikin hanyar. Garba Pella yace an baiwa kamfanin hydro source and resource Nigeria limited aikin hanyar a kan kudi naira miliyan dari takwas da sittin, da dubu dari takwas da ashirin da biyu da Naira dari

Babban sifeton Yan sandan Najeriya ya ziyarci jahar Adamawa

Image
. Babban sifeton yan sandan Najeriya Kayode Adeolu Egbetokun ya ziyarci jahar Adamawa domin jajantawa da nuna alhinisa dangane rikici da ya shiga tsakanin sojoji da yan sanda a kwanan nan lamarinda yayi sanadiyar mutuwar Jami in Dan sanda Daya wato isfeta Daniel Jacob. .Kayode Adeolu ya kuma gana da masuruwa da tsaki da suka hada da gwamnan jahar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri da Mai martabar Lamidon Adamawa Dr Barkindo Aliyu Mustafa. Kakakin rundunan yan sandan a Najeriya ACP Olumuyiwa Adejobi ne ya baiyana haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Abuja A yayin ziyaran Babban sifeton yane hadin kai a tsakanin rundunan yan sandan da gwamnatin jahar jarma da sarakunan gargajiya dake fadin jahar a wani mataki na inganta tsaro domin magance matsalar tsaro da suka addabi jama a.

Gwamnatin jahar Adamawa yace bazatayi kasa a gwiwaba wajen goyon bayan rundunan yan sanda.

Image
Gwamnan jahar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri yace gwamnatin shi za ta ci gaba da baiwa rundunar yan sanda goyon baya da take bukata domin bata damar sauke nauyin gudanar da aiyukan kare rayuka da kadarori a jahar. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri ya baiyana hakane yayin da ya karvi bakoncin babban sifeto janar na yan sanda, sKayode Egbetokun, wanda ya ziyarci shi yayin da ya ke ziyaran aiyuka a birnin Yola, fadar jahar Adamawa . Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri yace , rundunar yan sandan jahar na kokari matuka gurin kare rayuka da kaddarorin al'ummar jahar Kuma komishinan yan sandan jaha, CP Tola Afolabi na da kokari matuka. A cewar gwamna fintiri, komishinan yan sandan na kokari gurin hada kai da sauran takwarorin shi na jahar wanda abun yabawa ne kuma zai cigaba da bashi goyon

Babban sifeton yan sanda Najeriya ya jadda da aniyar rundunan na cigaba da hada kai da sauran hukumomin tsaro wajen kare rayuka dama dukiyoyin Al umma.

Image
Biyo bayan rikici da aka samu kwanan nan a tsakanin yan sanda da sojoji lamarinda yayi sanadiyar mutuwar wani isfeto wato Daniel Jacob. Babban sfeton yan sandan Najeriya Kayode Adeolu Egbetokun ya kawo ziyara jahar Adamawa a wani mataki na jajjantawa dangane da mutuwar Jami in dan sandan. A jawabinsa da ya gudanar a wurin taron jamin an yan sandan da aka gudanar a shelkwatar rundunan yan sandan a jahar Adamawa Babban sifeton yan sandan ya nuna damuwarsa dangane da aukuwar lamarin tare da yin fatan lamarin maikama da wannan ba zai sake faruwa ba a fadin Najeriya. Babban sifeton ya kuma jaddada aniyar rundunan na cigaba da hada kai da sojojin dama sauran hukumomin tsaro domin ganin a

Gwamnatin jahar Adamawa ta amince da Karin dubu goma na alawus alawus din masuyiwa kasa hidima a jahar Adamawa

Image
Gwamnatin jihar Adamawa ta amince da karin Naira dubu goma kan alawus alawus na matasa masu yi wa ƙasa hidima da aka turo jahar daga watan Janairun 2024. Gwamnan jahar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri ne ya sanar da haka yayin bikin rantsar da matasan na 2023 , rukunin 'BA' tawaga ta biyu wadanda aka turo jahar Adamawa, da ya wakana a sansanin horar da su da ke yankin damare na ƙaramar hukumar Girei. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri yace wannan karin kudi da akayi an yi shine domin rage radadin cire tallafi man fetur da gwamantin taraiya ta yi. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri ya ce babu kuskure gurin turo daliban jahar Adamawa domin yi wa ƙasa hidima, hakan na nan ciki jerin manufofin hukumar na karawa matasan masaniya kan irin taruka da al'adu da ake da su a fadin kasa, a kuma fahimtar da su domin bada tasu gudummawa gurin hadin kai, zaman lafiya da ci gaban k

Attarahum Foundation Distribute Food items to over forty Vulnerable in Adamawa.

Image
Attarahum Foundation has distributed Food items to over forty two Vulnerable people in Adamawa state in order to reduce hardship among the communities in the state. In his speech during the distribution of the items, Chairman Attarahum Foundation Adamawa state chapter Mallam Mukhtar Dayyib said the essence of distributing the items is to assist the vulnerable people in the society, in line with the aims of the Foundation. He said the Foundation has done many things to reducing hardship in the society for the development and peaceful coexistence among the communities in the state and the country at large. He also advised the beneficiaries to rightly utilize what was given in the right way for the development and unity among the people. Mallam Mukhatar Dayyib urged the Federal and state government t

Gidauniyar Attarahum ta rarraba kayakin abinci wa mutane Sama da arba in a jahar Adamawa.

Image
Gidauniyar Attarahum ta rarraba kayakin abinci wa marassa galihu sama da arba in a jahar Adamawa domin su samu sauki rayuwa duba da yanayi da ake ciki na matsalar rayuwa. Da yake jawabi a lokacin rarraba kayakin shugaban Gidauniyar Attarahum a jahar Adamawa Mllam Mukhtar Dayyib yace sun dauki matakin hakane domin ragewa Al umma radadin wahalar rayuwa da ake ciki a halin yanzu. Mallam Mukhtar Dayyib yace daman manufofin Gidauniyar shine taimakawa gajiyayyu, da marayu, Kuma basu yakaita ga musulmai kawaiba harma da mabiya addinin kirista ma suna taimaka musu. Mallam Dayyib ya Kara da cewa kawo yanzu Gidauniyar tana da rassa a dukkanin kananan hukumomi ashirin da Daya dake fadin jahar ta Adamawa. Kuma sun dauki matakin Bude rassanne domin fadada aiyukansu na taimakawa Al umma. Ya Kuma kirayi gwamnatin tarayya Dana jahar da sukasance suna taimakawa mabukata a Koda yaushe dom

Gwamnonin shiyar Arewa masau gabas sun lashi takwabin gudanar da aiyukan cigaban yankin.

Image
Gwamnonin yankin arewa maso gabashin Najeriya sun baiyana bukatar hadin kan yankin, yayin da kungiyar gwamnonin na arewa maso gabas ta yanke shawarar aiki tare da kamfanin wutan lantarki na Shanghai domin gina cibiyar wutan lantarki mai amfani da coal da zai bada wuta mai karfin megawatt sittin , ko mai amfani da karfin rana da zai bada wuta mai karfin megawatt hamsin domin shawo kan matsalar wutan lantarki a yankin. Daukan wannan maataki na kunshe ne cikin jerin matakan da kungiyar gwamnonin ta dauka a kaeshen zaman ta karo na tara da tayi a birnin Yola, fadar jahar Adamawa. Wadannan matakai wanda gwamnan jahar yobe , Mai Mala Buni ya karanto a madadin takwarorin shin a yankin yace , sun cin ma matsayar cewa ko wace jaha ta dau wannan batu na hadin kai da muhimmanci, ta hanyar daura hakkin tabbatar da hakan a wuyan babban jami’i. Yayin da

Makarantar NAFAN ta shiryawa daluben Firamare gasar wasanni a wani mataki na kara musu kwarin gwiwar wajen karatu.

Image
A wani mataki na karawa yara kwarin gwiwa karatu domin su samu inganceccen ilimi hakan yasa makarantar NAFAN Academy ta shiryawa daluben makarantar firamare wasanni a tsakanin daluben makarantar. Wasannin da an dauki kwanaki biyar ana gudanarwa wanda kuma an gudanar da wasanni daban daban da suka hada da wasan tsare, fareti, tsalle, da dai sauransu. Bikin kammala wasannin dai ya samu halartan shugaban makarantar Alhaji Adamu Jingi wanda akafi sani da maihange tare da iyalensa dama shuwagabanin makarantar sakandare dana kwalejin kimiya kiwon lafiya, da kuma mataimakin short gaban kungiyar malamai ta kasa N U T shirya karamar hukumar yola ta arewa. Da yake jawabi shgaban makarantar Alhaji Adamu Jingi ya baiyana godiyarsa dangane da shirya wannan gasa tare da kiran iyaye da su

NDIC sensitised secondary schools students. on saving in Adamawa.

Image
By Ibrahim Abubakar. Nigeria Deposit Insurance Corporation (NDIC) has sensitised no fewer than 100 secondary school students in Adamawa about the significance of savings for better tomorrow. The corporation’s Zonal Coordinator in Yola, Victor Egba, said during the sensitisation on Thursday that the programme was to inculcate saving culture among students in commemoration of this year’s World Savings Day. Our correspondent reports that the day is annually celebrated on Oct. 31 to raise awareness about the importance of savings, and has “Conquer Your Tomorrow Through Savings” as the theme for 2023. Egba, therefore, said that “the main target is to make students to start planning on how and where to save their monies for the future. “One of the rationale for establishing NDIC is to protect depositors’ funds in banks; so that in the event of fail

Hukumar NDIC ta shiryawa dalube taron fadakarwa dangane da ajiya a Bankuna a jahar Adamawa.

Image
Daga Ibrahim Abubakar. A yayinda aka gudanar da ranan Adana ta duniya hukumar inshoran Bankuna a Najeriya wato NDIC ta shirya taron wayarwa daluben makarantar gaba da firamare a kalla 100 kai dangane da yadda zasu kasance suna ajiyar kudinsu domin inganta rayuwarsu. Da yake jawabi a wurin taron ko odinatan hukumar a shiyar yola Victor Egba yace makasudin shiryawa daluben wannan taron dai shine wayarwa daluben kai dangane da muhimmanci ajiya a banki wanda hakan zai tamaka musu wajen tafiyar da rayuwarsa yadda ya kamata. Wakilin Al Nur ya rawaito cewa a ranan 31 ga watan oktoba ne dai ake gudanar da bikin ranan adana ta duniya domin nuna irin muhimmanci ajiya ke dashi. Egba ya kara da cewa aniyar hukumar dai itace fadakar da daluben yadda zasu kasance suna ajiyar kudinsu a bankuna domin kare martabarsu. Domin yana daya daga cikin manufo

Man 53 Arrested for Allegedly sexual Assault on minor in Adamawa state.

Image
As their effort to takle issue of sexual Assault in the state Adamawa state police Command Arrested 53year old Suspect identified as Usman Tela Ahmadu, a resident of Samunaka, Yola sauth Local Govement Area have been arrested for Sexually Assaulting a Mentally Challenged Minor. Adamawa state police relation officer SP Suleiman Yahay Nguroje stated this in a statement made available to Newsmen in Yola. The Suspect, hails from Maiduguri in Borno State and resides in the Area as an internally displaced person (IDP) receiving gifts and undue support/ sympathy from the Locals. The suspect further reveals he sexually assaulted the Mentally Challenged Girl four times started year 2021. The Commissioner of Police, CP Afolabi Babatola, while expressing Worries Calls on Parents/Guardians to live up to expectation in providing Necessity to th

Rundunan yan sandan jahar Adamawa tana tsare da wani Mai shekaru hamsin da ake zargi da cin zarafin karamar yarinya.

Image
A kokarinta na dakile aikata cin zarafin yaran mata a fadin jahar rundunan yan sandan jahar Adamawa tana tsare da wani mutum Mai shekaru 53 Mai Suna Usman Tela Ahmadu mazaunin samunaka dake cikin karamar hukumar yola ta kudu a jahar Adamawa bisa zarginsa da yiwa wata yarinya Mai fama da tabin hankali fyade. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da rabawa manema labarai a Yola. Wanda ake zargi da ya fitone da Maiduguri dake jahar Borno inda yake zaune a wurin a matsayin dan gudun hijira wanda Kuma Yana samu taimako daga jama a. Bincike ya nuna cewa Wanda ake zargin Yana cin zarafin yarinyar da take fama da tabin hankali tun daga shekara ta 2021. Kwamishinan Yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola ya baiyana damuwarsa dangane da aukuwar lamarin tare da shawartan iyaye da sukasance suna maida hankali kan yaransu a

Gov. Fintiri meets security chiefs sues for peace.

Image
Governor Ahmadu Umaru Fintiri of Adamawa State has summoned an emergency security meeting over Tuesday’s night clash between the military and police officers in the state. The conflict between the security personnel has begun along Target Junction, Yola North Local Government Area, that resulted in exchange of fire and Brutal attacked on the Police Facility. Addressing newsmen after the meeting in the Government House, Yola Wednesday, Governor Fintiri said an investigation into the matter was ongoing with a view to ensuring peace and justice. He said the meeting has resolved the conflict and that the security chiefs have vowed to work in synergy for the best interest of Adamawa and Nigeria. Governor Fintiri confirmed that both the military and police lost one officer each during the night clash, calling for restrain to avoid recurring such incident. The meeting had in attendanc

Gwamnan jahar Adamawa ya tattauna da sojoji da yan sanda biyo bayan rashin jituwa da aka samu a tsakaninsu.

Image
Biyo bayan rikici da aka samu a tsakanin sojoji da yan sandan a jahar Adamawa. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jahar Adamawa ya gudanar da taro da sojoji da yan sandan domin kawo karshen matsalar. Da yake yiwa manema labarai jawabi Jin kadan da kammala taron a gidan gwamnati dake Yola, Gwamna Fintiri yace za a gudanar da bincike dangane da lamarin domin tabbatar da zaman lafiya da adalci. Yace tattaunawa ya warware matsalar harma hukumomin tsaron sunyi alkawari yin aiki tare domin kare rayuka dama dukiyoyin Al ummar jahar da kasa baki Daya. Gwamna Fintiri ya tabbatar da cewa dukkanin bangarorin biyu sun rasa Jami ansu Daya Daya a lokacin rikicin tare da kira da sukasance suna Kai zuciya nesa domin kaucewa sake aukuwar wannan matsalar. Rikici a tsakanin hukumomin tsaron dai ya fara ne daga Mahadar taget dake cikin karamar hukumar yola ta arewa a jahar Adamawa.

Wani jami in dan sanda ya rasa ransa sakamokon rikici a tsakanin sojoji da yan sanda a jahar Adamawa.

Image
Kwamishina yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola yayi Allah wadai da rikici da faru a tsakanin yan sandan da sojoji a Target Junction cikin karamar hukumar yola ta arewa biyo bayan musayan harbe harbe da sukayi a tsakaninsu lamarin da yayi sanadiyar mutuwar wani Jami in dan sanda mai mukamin isfeto. Kakakin runduna yan sandan a jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya baiayan haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a yola. Kwamishinan yan sandan tunin ya bada umurni da a gaggauta gudanar da bincike dangane da lamarin. Sanarwan ta kuma baiyana cewa kwamshina ya baiyana ta kaicinsa lamarin da yace abin takaicine ace ana samun irin wadannan hare hare a tsakanin hukumomin tsaro Jami an da suke gudanar da aiyukansu domin kare rayuka dama dukiyoyin al umma kuma sannan ace ana kai musu hari wannan ba daidaibane. Ya kuma jadda aniyar rundunan na

Majalisar dokokin jahar Adamawa ta amanice da sunayen shuwagabanin gundumomin raya yankuna dake fadin jahar.

Image
Majalisar dokokin jahar Adamawa ta amince da sunayen mutane hamsin na shuwagabanni gundumomin raya yankuna da sakatarorinsu a jahar Adamawa. Amincewar ya biyo bayan wasikar bukatar amuncewa da sunayen da gwamna Ahmadu Umaru Finti ya akewa majalisar wanda kakakin majalisar dokokin jahar Adamawa Bathiya Wesley ya karanta a zauren majalisar a zamanta da tayi a ranan litinin. Dan majalisa mai wakiltan karamar hukumar Maiha Ahmed Jingi Belel ne ya taso da batun amincewa da sunayen shuwagabanin gundumomin raya yankin da sakatarorinsu wanda ya samu goyon bayan memba mai wakiltar Verre Japhet Hammanjabu. Daga nan sai kakakin majalisar Bathiya Wesley ya umurci akawun majalisar da ya gabatarwa majalisar zantarwar jahar batun amincewar domin daukan mataki na gaba.

Rundunan yan sandan jahar tana tsare da wani da ake zargi dayiwa yar shekaru biyar fyade.

Image
Rundunan yan sandan jajar Adamawa a kokarinta na dakile cin zarafin yara yanzu haka tana tsare da wani wanda ake zargi da yiwa wata yarinya fyade a karamar hukumar Mayo Belwa dake jahar Adamawa. Kakakin rundunan yam sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya naiyana haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a yola. Sanarwan tace rundunan ta samu koke da wani magidanci mai suna Adamu Ahmed mazaunin Dikon Nasarawa a karamar hukumar Mayo Belwa cewa anyiwa yarsa mai shekaru biyar fyade. Daga jin wannan labari kwamishina yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola baiyi da wasaba. Tunin ya umurcin Jami an yan sandan dake Mayo Belwa da su gudanar da bincike kan lamarin domin tsare wanda ake zargi da aikata fyaden. Bisa bincike da aka gudanar dai yanzu haka ana tsare da wani mai suna Musa Inusa mai shekaru talatin da ake zarg

An yabawa Yan jaridan gidan gwamnati bisa kokarin su na fadakar da Al umma dangane da aiyukan gwamnatin jahar.

Image
Gwamnan jahar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri ya baiyana godiyar shi wa yan jarida da masu harkar yada labarai na jahar bisa gudummawar da suke bayarwa gurin kare danokradiya a jahar. Governor Ahmadu Umaru Fintiri ya yi wannan godiya ne yayin wani buki na musamman da akayi wa lakabi da bukin nasara , wanda aka shirya wa yan jarida musamman wadanda suke aiki a gidan gwamnati a hutun karshen mako, da suka kasance da gwamnan tun wa' adi na farko har zuwa yanzu. Governor Ahmadu Umaru Fintiri, wanda ya samu wakilcin shugaban ma'aikatan gidan gwamnati, Dakta Edgar Emos Sunday yayin bikin ba za a iya misalta irin gudunmawar da yan jarida ke bayar wa a jahar ba, musamman wadanda suka gudanar da aiyukan su a gidan gwamnati , wannan ne ya sa aka shirya wannan buki domin jinjina musu gurin kokarin daidai ta harkokin danokradiya a jahar. Governor Ahmadu Umaru Fintiri yace gwamnatin shi na matukar

Rundunan yan sandan Najeriya tana daf da rufe shafin diban jami an yan sanda.

Image
Rundunan yan sandan Najeriya tace duk da cewa ana daf da rufe shafin yanan gizon diban Jami an yan sanda kawo yanzu runduna ta samu wadanda suke bukatar shiga aikin yan sandan sunkai dubu dari biyar da arba in da bakwai da dari bakwai da saba in da hudu.547,774. tunda aka bude shafin tun daga ranan 15-10-2023. Wanda kuma za arufe a ranan 26-11-2023. Mr Ikechukwu Ani shine Jami in watsalabarai sashin diban Jami an yan sandan ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar. Sanarwan ta baiyana cewa cikin mutane 547774 wadanda suka bukaci shiga aikin yan sanda 358,900 ne suka samu nasaran shiga zagaye na farko biyo bayan gwaje gwaje da aka yi musu na kiwon lafiya da dai sauransu. A yayinda 84,606 kuwa basu samu shigaba duba da matsaloli da aka samu da suka hada da yawan shekaru, saboda ana bukatar wadanda shekarunsu suka kama daga 18-25. Kawo yanzu dai jahar Kaduna itace na

NNPP concluded the Arangement to paticipate LG polls in Taraba.

Image
By Sani Yarima Jalingo Ahead of the Saturday local government council's polls, the New Nigeria People's Party NNPP in Taraba State says all is set for the party to go into contest. The State Chairman of the party, Hon. Abdullahi Ade made this known while fielding questions from journalists in his office in Jalingo. He said the party has already necessary arrangements have been concluded including the provision of Agent's tags. According to Hon. Abdullahi Ade, they have six (6) candidates that will contest for the chairmanship at six local government areas of the state comprising Jalingo, Ibi, Yerro, Karim Lamido, Gassol, and Sardauna. For the councilorship, the Chairman further revealed that the party has about forty candidates that contest across the sixteen LGAs of the state. Commenting on the recent endorsement of the People's Democratic

Jam iyar NNPP dake jahar Taraba tace ta kimtsa tsaf domin shiga adama da ita a zabukan kananan hukumomi dake fadin jahar.

Image
Daga Sani Yarima Jalingo A yayinda ake daf da gudanar da zabuka a dukkanin kananan hukumomi jahar Taraba Jam Iyar NNPP a jahar Taraba ta kammala dukkanin shirye shirye da suka kamata domin tunkaran zaben dake tafe a jahar . Shugaban Jam Iyar NNPP a jahar Taraba Alhaji Abdullahi Ade ne ya baiyana haka a lokacinda yake amsa tambayoyin Yan Jarida a ofishinsa dake Jalingo fadar gwamnatin jahar Taraba. Ya dukkanin shirye shirye da suka kanata da suka hada da yin katin shaidar wakilainsu na runfunan zabe wato Tags duk suyisu. A cewarsa dai kawo yanzu suna da Yan takaran shuwagabanin kanana hukumomi shida da suka hada da Jalingo, Ibi, Yerro, Karim lamido, Gassol, da Kuma Sardauna. Dangane da Yan takaran kansiloli kuwa sai shugaban ya baiyana cewa suna da Yan takaran kansil

Rundunan yan sandan Najeriya ta taimakawa magadan jami anta da suka mutu a bakin aiki.

Image
Rundunan yan sandan Najeriya ta baiwa magadan jami an yan sanda da suka gamu da ajalinsu a lokacinda suke gudanar da aiyukansu na kare Martaban kasa . Babban sifeton yan sandan Najeriya Kayode Adeolu Egbetokun ne ya kaddamar da bada cek din kudaden ga iyalen marigaya karkashin tsarin nan dake kula da walwalan Jami an yan sanda inda iyale 613 ne suka amfana da tallafin biyo bayan mutuwar yan uwansu a cikin shekaru da suka kama daga shekara ta 2020/2021 da 2021/2022 sai kuma 2022/2023. Da yake jawabin a wurin bikin tallafin da ya gudanar a shelkwatar rundunan yan sandan dake Abuja. Babban sifeton yan sandan ya baiyana irin muhimmanci da irin wannan taimako yake dashi domin rundunan ta kudiri aniyar kula da walwalan dukkanin Jami anta a koda yaushe kama daga wadanda suka rasa rayukansu a bakin aiki ko kuma wadanda sukati ritaya. Hakan na knshene a cikin wata sanarwa daga

Gwamnan jahar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri yace gwamnatinsa na samun goyon baya daga kungiyoyi dake fadin jahar.

Image
Gwamnan jahar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri yace gwamnatin shi na baiwa goyon bayan da take samu daga kungiyoyi da ke fadin jahar muhimmanci musamman irin kungiyar mabiya addinin krista na CAN domin ci gaban jahar. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri ya baiyana haka ne yayin da ya karbi bakoncin jagororin kungiyar mabiya addinin krista, CAN karkashin jagorancin shugaban ta, Rabaren Dami Mamza wadanda suka zo gidan gwamnati ziyara. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri ya bada tabbacin cewa yan jahar za su yi urmushi ganin gwamnati na aiyukan saita lamarori da zasu tabbatar da inganta rayuwan su. Gwamnan yace labara na sauyawa a dukkan fannoni dake jahar, musamman a bangarorin ilimi da tsaro ganin a yanzu jahar nan a biyu a jarrabawan kammala sakadandare na NECO da WAEC, kuma ana ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’ummar jahar, sabannin yaddaa lamarin ke nan shekaru hudu d

Hukumar raya yankin arewa masau gabas ta gamsu da yadda aiyukan ke tafiya a yankin na arewa masau gabas.

Image
Sabbin nadaddun mambobin hukumar ci gaban yankin arewa maso gabas, wato NEDC sun kai ziyarar ban girma a fadar mai martaba lamidon Adamawa. Shugaban hukumar, Manjo Janar Paul Tarfa ma I ritaya yace a kwai bukatar ziyaran yankin, a kuma gana da masu ruwa da tsaki da kuma gabatar da mambobin hukumar tare da Karin hasken nasarori da hukumar da cin ma. Shugaban hukumar ya kara da cewa sun zo jahar Adamawa ne domin duba wasu aiyuka da akeyi a jahar, su kuma san inda aka dosa domin gi gaban hukumar. Ya yaba da kokarin mai martaba Lamidon Adamawa na tabbatar da zaman lafiya tare da mika bukatan addu’oi da shawarwari domin ci gaban hukumar da ma yankin are maso gabashin Najeriya baki daya. Da yayi jawabi, mai martaba Lamidon Adamawa, dakta Barkindo Aliy Mustafa wanda Galadiman Adamawa, Mustafa Aminu ya wakilta yayin ziyara

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jahar Adamawa yace jahar tana murmurewa sakamokok rikicin Boko haram.

Image
Gwamnan Jahar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri yace jahar na kan farfadowa daga illar hare haren yan ta’adda a yankin na arewa maso gabas. Gwamnan Ahmadum Umaru Fintiri ya baiyana haka ne yayin da ya karbi bakoncin mambobin hukumar ci gaban yankin arewa maso gabas da aka sake nadawa a lokacin da suka kawo ziyara a ofishin shi cikin aikan su na zaiyar duba aiyuka a yankin na arewa maso gabas. Gwamnan Ahmadu Umaru Fintiri yace har yanzu akwai wasu kanana hukumomi da hanyoyi da gadajen su na bace sakamakon hare haren yan ta’adda. Gwamnan ya kuma koka da dabi’un yan kwangila da suka gaza aiwatar da aiyukan su a jahar bayan amincewa ta kwangilar, wanda acewar shi hakan ya taimaka gurin jefa mutane cikin mawuyacin hali. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri ya gode wa tawagar da wannan ziyara tare jinjina wa hukumar da irin aiyukan ci gaba da take aiwatarwa musamman a jahar ta Adamaw

Babban sifeton yan sandan Najeriya ya yabawa hukumomin tsaro.

Image
Babban sifeton yan sandan Najeriya Kayode Adeolu Egbetokun ya yabawa dukkanin Jami an yan sandan Najeriya dama sauran hukumomin tsaro bisa rawan da suka taka wajen inganta tsaro a lokacin zabe gwamnonin da aka gudanar a jihohin Bayelsa, Imo da Kuna jahar Kogi. Kakakin rundunan yan sandan ta kasa ACP Olumuyiwa Adejobi ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar a Abuja Sanarwan ta baiyana cewa Babban sifeton Yan sandan yace Jami an Yan sandan dama sauran hukumomin tsaro sun yaka rawan gani wajen bata tsaro Dama kariya a lokacinda ake gudanar da zabukan. Babban sifeton yace zaben da ya gudana a jihohin uku ingancaccen zabe ne Wanda Kuma hakan ya biyo bayan tsayin daka da jami an tsaro aukayi wajen kare masu kada kuri a domin tabbatar da cewa sunyi zabe cikin kaunciyar hankali ba tare da matsalaba. A Daya hanun Kuma dangane da matsàloli da suka faru

NNPP in Taraba State is ready to paticipate LG Polls in Taraba.

Image
By Sani Yarima in Jalingo As the local government councils election is around the corner, the Taraba State Chairman of the New Nigeria People's Party (NNPP), Hon. Abdullahi Ade has expressed optimism that the election will be free and fair Ade aired this pronouncement while briefing newsmen in Jalingo, the capital city of the state. He said their party, the NNPP had agreed to take part in the election because of the assurances that the Chairman of the TSIEC, Dr. Phillip Duwe gave all the political parties in the state of conducting a free, fair, and credible election. "We have been meeting with the TSIEC Chairman, Dr. Danladi Phillip Duwe, he called us frequently since they released the timetable for the LG Council polls, I think we have met almost five times and he promised us that the commission would conduct a free and fair election which I always quote him by his words, and I am optimistic

Jam iyar NNPP a jahar Taraba ta baiyana aniyarta shigaba zabukan kananan hukumomi a fadin jahar.

Image
Daga Sani Yarima Jalingo A yayinda zaben kananan hukumomi ke karatowa. Shugaban jam iyar NNPP a jahar Taraba Hon. Abdullahi Ade ya jadda cewa zaben kananan hukumomin zai gudana cikin inganci. Ade ya baiyana hakane a lokacinda yake yiwa manema labarai jawabi a Jalingo Fadar gwamnatin jahar ta Taraba. Yace jam iayarsu ta NNPP ta amince zata shiga a dama da ita acikin zaben kananan hukumomi duba da yadda shugaban hukumar zaben jahar Taraba wato TSIEC Dr Danladi Phillip Duwe ya tabbatar da cewa dukkanin jam iyun siyasa jahar suna da daman shiga zaben kuma za a gudanar da zabe mai inganci. Ya ce mun gudanar da taro da shugaban hukumar zaben na jahar Taraba Dr Danladi biyo bayan gayyatanmu da yayi bayan an fitar da jadawalin zaben kananan hukumomi kuma muyi taro akalla ya kai sau biyar tare da yi mana alkawarin cewa hukumar zata gudana

Gwamnatin jahar Adamawa ta kirayi gwamnatin tarayya da ta Samar da madatsar ruwa a Dasin domin kaucewa Ambaliyar ruwa.

Image
Gwamnan jahar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri ya kirayi gwamnatin taraiya data samu mafita mai daurewa domin kawo karshen ambaliya da ake fama da shi a fadin kasa. Gwamna Ahamadu Umaru Fintiri yayi wannan kira ne a lokacin da ya karbi bakoncin babban daraktan hukumar bada agajin gaggawa ta kasa, NEMA Mustapha Habib Ahmed da wasu jami’an hukumar yayin da suka kawo ziyara a ofishin shi da ke gidan gwamnati a Yola. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri yace cikin matakan shawo kan matsaloli da ake fuskanta yayin ambaliya akasa, ya kamata gwamnatin taraiya da gina wani dam a dasin hausa, wanda a cewar shi hakan zai taimaka gurin rike ruwa da ake sako wa daga Lagdo dam na kamaru wanda ke kawo ambaliya ko wani shekara, kuma matsalar ya shafan jahohi da dama a fadin kasa. Gwamna Fintiri yace ya kamata gwamnatin taraiya ta baiwa gina wanna dam din muhimmaci, ganin yin hakan zai taimaka gurin bukasa harkok

ANWBN Urge Taraba State government to boost Business in the State.

Image
By Sani Yarima in Jalingo The Association of Nigeria Women Business Network ANWBN, has appealed to the Taraba State government to allocate stores for market women in the informal sector. Advocacy Chair, ANWBN, Foluke Ademokun made the plea at a meeting organized by the TinT- Follow Taxes in partnership with the International Budget Partnership (IBP) held at Fast Track Hotel in Jalingo. The two-day meeting aimed to identify and address gaps in the implementation of existing framework and policies, Tax codification, harmonization policy, and internal control measures. The objective was also to identify and specify the taxes that informal sector businesses are obligated to pay and their corresponding rates. The ANWBN says "The expectation is now that government should look at the allocation of stores because we have more women as traders. If we have more market women than market men of course we should see that wome