Posts

Showing posts from January, 2023

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta shiyar B tace tayi nasaran kama mutane akalla dari tara da saba in da bakwai a shekara ta 2022.

Image
Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi a Najeriya N D L E A shiyar B Wanda ya kunshi jihohi Adamawa, Taraba da kuma jahar Gombe tace tayi nasaran kama mutane dari Tara da saba in da bakwai wadanda ake zargi da safaran miyagun kwayoyi a Yankin na B. Kwamadan hukumar a yankin na B Alhaji Idris Bello ne ya baiyana haka a lokacin da yake Zantawa da jaridar Al Nur a yola, dangane da irin nasarorinda hukumar ta N D L E A tayi a shekara ta dubu biyu da ashirin da biyu a yankin. Kwamandan yace cikin wadanda aka kama dari tara da saba in da bakwai wadanda suka hada da mata an yankewa dari uku da sittin da biyar hukunci a yayinda dari uku da saba in da hudu kuma an basu shawarwari domin su daina ta ammali da miyagun kwayoyin. Alhaji Idris Bello ya kuma baiyana cewa hukumar tayi nasaran kama miyagun kwayoyi da nauyinsa yakai kilo grama milyon biyu da dubu dari bakwai da hamsin da bakwai da dari tara da saba in da uku. Wato 2,757,973. Da wannan ne kwamandan

An yaba da shugabanci shugaban karamar hukumar Girei dake jahar Adamawa.

Image
An yabawa shugabancin karamar hukumar Girei dake jahar Adamawa Hon. Juda Amisa garkuwar Luru tafida. Tambo. bisa yadda yake gudanar da aiyukan cigaban karamar hukumar dama cigaban karamar hukumar. Muhammed Muratalan ya yi wannan yabo a lokacinda ya zantawa da jaridar All Nur a yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Muhammed Murtala yace Him. Juda ya gudanar da aiyukan cigaban Al ummar karamar hukumar ta Girei a bangarori daban daban da suka hada da gina asibitoci, makarantu, Bohol Bohol, hanyoyi, bunkasa harkokin noma, da kiwo zaman lafiya da dai sauransu. Murtala ya kuma baiyana cewa Juda mutumne da ya san makaman shugabanci saboda yayi kansila har sau biyu ya rike mukamin shuhaban majalisar kasinlolin karamar hukumar ta Girei, ya kuma yi mataimakin shugaban karamar hukumar Girei haka kazalika ya yi shugabancin karamar hukumar Girei sau biyu, saboda haka ya kware wajen gudanar da shugabanci da kuma gudanar da aiyukan cigaban Al ummah. Don haka n

An bukaci iyaye su kara kaimi wajen tura yaransu islamiyoyi.

Image
An ja hankalin iyaye da su maida jankali wajen tura yaransu makarantu domon koyon karatun Al qur ani maigirma domin ganin an samu cigaban karatun al qur ani a tsakanin yara baki daya. Alhaji Sadiq Umar Daware ne yayi wannan kira a lokacin da yake jawabi a wurin bikin kammala gasar karatun Al qur ani maigirma wanda Gaskiya TV afirka ta shirya a yola. Alhaji Sadiq Daware shinema shugaban taron yace koyar da yara karatun Al qur ani tun suna yara yana da matukan muhimmanci don haka yakamata iyaye su tashi tsaye wajen baiwa yaransu ilimin karatun Al qur ani domin samun cigaban addinin musulunci. Ya kuma yabawa kungiyar ta gaskiya TV da ta shirya wannan gasa kuma ya kirayi sauran kungiyoyin addinin musulunci da su cigaba da shirya irin wannan gasa wanda acewarsa hakan zai taimaka wajen bunkasa ilimin addini da ma karatun Al qur ani maigirma. Ya Kara jaddada goyon bayansa a duk lokacin da aka bukaci taimakonsa tare da shawartan al umma musulmai da sukasance masu

Kungiyoyi dari biyar ne suka kudiri aniyar ganin Alhaji Atiku Abubakar yayi nasara a zabe mai zuwa.

Image
A kalla kungiyoyi Nagoya bayan Atiku dari biyar ne sukayi rijista domin ganin Alhaji Atiku Abubakar yayi nasara a Babban zaben shekara ta dubu biyu da ashirin da uku. Ko odinatan Atiku Mandate na kasa Alhaji Sa idu Komsari ne ya baiyana haka a wajen taron shuwagabain kungiyoyin da aka gudanar a yola. A taron dai kungiyoyin sunyi Alwashin ganin dan takaran shugaban kasa a jam iya P D P Alhaji Atiku Abubakar ya lashe zaben shugaban kasa a zabe mai zuwa. Kungiyoyin dai sun hada Kansu tare da nuna jindadinsu da shirya wannan taro Wanda hakan ya nuna cewa wazirin Adamawa zai kai ga samun nasara. Don haka Alhaji Sa idu Komsiri ya kirayi kungiyoyin da su tabbata sunyi aiki kafada da kafada da sauran kunyoyin domin ganin an samu nasara a Babban zaben. Ya kuma kirayin yan Najeriya da su hada kai su baiwa Alhaji Atiku Kuri u wanda hakan zai taimaka ya samu damar lashe zaben sjekara ta 2023. An dai gudanar da jawabai daban daban a

An baiyana irin muhimmanci da karatun Al qur ani mai girma yake dashi a tsakanin al ummah musulmai.

Image
An kirayi Al ummah musulmai da su kara himma wajen gudanar da karatun All qur ani kai girma domin samun cigaban addinin musulunci yadda ya kamata a tsakanin Al ummah musulmai baki daya. Alhaji Sadiq Umar Daware ne yayi wannan kira a lokacinda yake jawabi a wurin bikin rufe gasar karatun Al qur ani mai girma wanda kungiyar gaskiya TV Africa shiyar jahar Adamawa ta shirya a yola. Alhaji Sadiq Daware wanda shine shugaban bikin yace karatun Al qur ani dama karantarwa yana da mutukan muhimmanci a tsakanin Al umma musulmai don haka akwai bukatan al umma musulmai sukasance masu runguman karatun Al qur ani domin samun daman yada addinin musulunci. Alhaji Daware ya kuma yabawa kungiyar ta Gaskiya TV bisa shirya wannan gasar karatun al qur ani mai girma ya kuma yi fatan zasu fadada aiyukansu har zuwa nahiyar Afirka baki daya. Ya kara kira ga al umma musulmai musammanma kungiyoyin addinin musulunci da suyi kasance masu shirya gasar karatun al qur ani ma

An horar da dalube harkokin wasanni daban daban a jahar Taraba.

Image
Daga Sani Yarima Jalingo. An shawarci musammanma dalube da sukasance masu neman ilimin wasan badminton domin su zama masu gudanar da irin wasanin a fadon duniya. Darectan wasannin jahar Taraba George Shitta ne ya bada wannan shawara a lokacin da yake jawabi a wurin bikin kamala horar da daluben sakandare wasan badminton da aka dauki tsawon kwanaki uku anayi a Jalingo fadar gwamnatin jahar Taraba. Dalube tamanin daga makarantun sakandare tamanin ne dai da suka da gwamnati harma da masu zaman kansu suka samu haron wasanni daban daban akalla ashirin da hudu. Shitta ya shaidawa manema labarai cewa wata kungiya mai zaman kanta wato kungiyar bunkasa wassani da ilimantarwa a cikin al umma CSED tare da hadin gwiwar sashin wasan badminton a jahar Taraba ne suka dauki nauyin. Yace sun dauki matakin horan da daluben ne domin zaburan da matasa dama bunkasa harkokin wassani a jahar ta Taraba. Darektan ya kuma yaba da yadda kung

Kungiyar Attarahum Faundation ta kaddamar da sabbin suwagabanninta nq kananan hukumomi.

Image
Kungiyar Attarahum Faundation dake jahar Adamawa ta kaddamar da shuwagabaninta na kananan hukumomi ashirin da daya dake fadin jahar Adamawa. An dai gudanar da taron kaddamawan ne a yola ta kudu a jahar Adamawa, wanda ya samu halartan Al umma dama da suka hada da yan siyasa da dai sauransu. Da yake jawabin maraba shugaban gidauniyar ta Attarahum Foundation a jahar Adamawa Mallam Muktar Dayyib ya baiyana dalilinsu na kafa wannan gidauniya domin taimakon kai da kai harma da taimakawa marassa galihu, marassa lafiya,marayu, gajiyayyu da dai sauransu. Wanda kuma hakan yasa suka ga ya dace su fadada gidauniyar zuwa kananan hukumomi wanda acewarsa hakan zai taimaka wajen cimma burinsu na taimakawa al umma baki daya. Don haka nema ya kirayi al umma da sukasance masu kafa irin wannan gidauniyar domin taimakawa jama a tare da shawartan masu hanu da shuni da suma su bada tasu gudumawa wajen tallafawa jama a. Malam muktar Dayyib ya yabawa yar takaran gwamnat

Zaben shekara ta 2023 kungiyar Atiku mandate tasha Alwashin gani Atiku ya samu nasara a zaben mai zuwa.

Image
Kungiyar Atiku Mandate ta sha Alwashin ganin Alhaji Atiku Abubakar ya samu nasara a Babban Zaben shekara ta dubu biyu da ashirin da uku. Ko odinatan kungiyar ta kasa Alhaji Sa idu komsari ne ya baiyana haka a zantawarsa da Jaridar All Nur a yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Alhaji Sa idu yace akwai tsare tsrea da dama da kuma matake masu yawa da sukayi wanda hakan zai taimaka wajen samun nasaran Alhaji Atiku Abubakar a zaben shugaban kasa wanda za ayi a shekara ta 2023. Alhaji Komsari ya kirayi daukacin yan Najeriya musammanma yan arewa da su sanifa wannan damace a garesu da su zabi Atiku wanda zai ceto kasan nan daga cikin matsaloli da ake fuskanta da suka hada da tattalin arziki, tsaro, da dai saraunsu. Ya kuma baiyana cewa wazirin wato Atiku Abubakar yana da kwarewa a fannoni daban daban kuma ya goge a fanin mulki da kasuwanci don haka akwai buiatan yan Najeriya su bashi hadin kai da goyon baya domin ganin ya samu nasara lashe zaben shu

An nada mace ta farko a matsayin waziriyar Song.

Image
An nada hajiya Aishatu Abubakar Ahmed Song a matsayin waziriyar Song wanda kuma itace mace ta farko da fadar hakimin song din ya ta a matsayin waziriya. An dai gudanar da bikin nadinne a fadar hakimin song wato Ahmed Sa idu wanda ya samu halartar yan uwa da abokan Arziki na ciki da wajen karamar hukumar Song dake jahar Adamawa. Da yake nadata hakimin na Song Ahmed Sa idu ya kirayi waziriyar da ta kasance mai baiwa masarautar hadin kai da goyon baya domin ganin samun cigaban masarautar dama hadin kan masarautar harma da al umar karamar hukumar dama jaha baki daya. Hakimin yace an nadatane biyo bayan irin gudumawa da take baiwa masarautar don haka ya shwarceta da ta kare martabarta dana masarautar domin samun cigaban masarautar harma da wanzar da zaman lafiya. Harwayau ya kirayeta da ta kasance mai nuna halaye ta gari a dukkanin lamuranta a koda yaushe dama cigaba da bada hadin kai da goyon baya ga masarautar wanda a cewarsa haka zai taim

Mazauna yankin gwalamba sun kirayi gwamnatoci a dukkanin matake domin gyara musu hanya.

Image
Mazauna yankin Gwalnba dake gundumar Lamtari a cikin karamar hukumar yola ta kudu sun krayi gwamnatin tarayya dana jahar harka dana kananan hukumar da su taimaka musu da gyara musu hanya, wutan lantarki cibiyar kiwon lafiya da dai sauran kayakin more rayuwa. Hardon gwalamba kuma mataimakin shugaba kungiya Pulaku Jamde Jam Foundation a jahar Adamawa Hassan Ali Soje ne yayi wannan kira a zantawarsa da Jarida Al Nur a yola. Hassan Ali Soja yace kiran gwamnatocin ya zama wajibi duba da irin yanayi da suke ciki na raahin hanya musammanma idan ake a damina yayi wanda da gomin goshi suke shiga da fita anguwar tasu ga kuma matsalar wutan lantarki wanda haka yayi sanafiya koma baya sosai a cikin unguwar tasu. A cewar Ali Soja da in har aka gyara musu hanya zasu samu damar bunkasa harkokin kasuwancin yankin kuma gwamatin zata samu kudin shiga. Saboda haka ya kamata gwamnatocin suyi dukkanin abinda suka dace domin suma su samu walwala yadda ya kamata. Ya

Kungiyar yan kasuwa na arewa sun goyi bayan Tinubu da Shetima.

Image
Kungiyara yan kasuwar arewacin Najeriya masu rajin goyon bayan Bola Ahmed Tinubu da Shetima a neman takaran shugaban kasa kakashin Jam iyar A P C a Babban zaben shekara ta dubu biyu da ashirin da uku. Ko odinatan kungiyar ta kasa Alhaji Adam Hassan Ibrahim ne ya baiyana haka a zantawarsa da Jaridar Al Nur ta waya inda yace dalilinsu na goyon bayan Tunibu da Shetima saboda Bola Tinubu ya gaji kasuwanci saboda haka in har ya samu nasara to yan kasuwa zasu samu tamogashi a fafin Najeriya. Alhaji Adam Hassan yace Tinubu ya gudanar da aiyukan cigaban a jaharsa wato Lagos a lokacin yana gwamna ya kuma taimakawa mutane da dama a sassa daban daban dake fadin kasan nan baki daya, don haka nema suka ga ya dace su marawa Tunibun baya domin ya kai ga samun nasara a zaben shekara ta 2023. Alhaji Hassan suna da yakinin cewa idan Bola Tunibu ya samu nasara zai maida hankali wajen bunkasa kasuwanci dama bunkasa tattalin arzikin kasa da kuma uwa uba matsalar

An shawarci yan agaji da sukasance masu taimakawa al ummah.

Image
An shawarci yan agajin fityanul Islam da sukasance masu taimakawa al umma a bangarori daban daban musammanma a bangaren kiwon lafiya domin samun cigaban yadda ya Kamata. Darektan yan agajin fityanul Islam na jahar Adamawa Alhaji Sa idu Modibbo Buba ne ya bada wannan shawara a lokacinda yake jawabi a wurin rufe taron karawa juna sanin wanda aka shiryawa yan agajin anan yola. Alhaji Sa idu yace an shirya wannan taronne domin karawa yan agajin sanin makaman aiki da kuma yadda zasu maida hankali wajen taimakawa al umma a bangarori daban daban. Ya kuma kirayi yan agaji da sukasance masu nuna da a a duk lokacin da suke gudanar da aiyukansu domin samun cigaban kungiyar a tsakanin al umma baki daya. Alhaji Sa idu ya kirayi yan Najeriya da sucigaba da yin adu oi domin neman taimakon Allah madaukakin sarki wajen kawo karshen kalubalen tsaro a fadin Najeriya baki daya.

Rundunan yan sandan jahar zamfara ta kama wadanda ake zargi da kaiwa yan bindiga makamai.

Image
A kokarinta na dakile aiyukan ta addanci a jahar Zamfara rundunan yan sandan jahar tayi nasaran kama wasu mutane biyu da ake zargi da safaran makamai wa yan bidigan a jahar ta zamfara. Kakakin rundunan yan sandan jahar Zamfara SP Muhammed Shehu ne ya baiyana haka a wata sanarwa da ya fitar a Gusau fadar gwamnatin jahar Zamfara. Sanarwan tace an samu nasaran cafke mutanenne akan hanyar Gusau Wanke Dansadau tare da albarushe har 325 da kuma binga kiran Ak 47 Wanda ake zargin dai sune Emmanuel Emmanuel ta da abokiyar aikinsa wato Nana Ibrahim. A cikin sanarwa an jiyo kwamishinan yan sandan jahar CP Kolo Yusuf ya tabbatarwa al umma jahar cewa rundunan a shirye take takare rayuka dama dukiyoyin al umma dake fadin jahar baki daya. Don haka nema ya ke kira ga daukacin al umma jahar da sukasance masu taimakawa rundunan da wasu bayanain sirri da zai baiwa rundunan yan sandan damar cika burinta na inganta tsaro a fadin jahar Zamfara baki daya.

An yabawa gwamnnatin tarayya dangane da karantar da daluben firamare harshen uwa.

Image
An yabawa gwamnatin tarayya bisa amincewa da a kararantar da daluben makarantin fimare da harshen uwa wanda hakan cigabane matuka. Alhaji Adamu Jingi yace gaskiya lamarin yayi dai dai wanda acewarsa ko kasashe da sukaci gaba a duniya suna karantar da dalubene da harshensu domon daluben su fahinci abinda ake koya musu yadda ya kamata. Don haka abinda gwamnatin tarayya tayi yayi dai dai kuma dafatan za a fadadashi zuwa makarantun gaba da firamare da kwalejoji harma da Jami o i domin hakane zai tai maka musammanma a bangaren likitoci, injiniyoyi, kimiya da fasaha da dai sauransu. Ya kuma kirayi masu ruwa da tsaki da sukasance masu bada hadin kai da goyon baya domin ganin gwamnatin ta cimma burinta na baiwa dalube inganceccen ilimi yadda ya kamata. Alhaji Jingi ya shawarci malamai makarantu musaman na firamare da su maida hankali sosai wajen karantar da dalube yadda ya kamata da kuma bin tsari

Hukumar zabe ta gamsu da yadda ake karban katin zabe a jahar Adamawa.

Image
Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC shiyar jahar Adamawa. ta baiyana gamsuwarta dangane da yadda al umma ke ta tururuwa zuwa karban Katin zabensu daga ofisoshin hukumar dake fadin jahar ta Adamawa baki daya. Mukaddashin kwamishinan hukumar zaben jahar Adamawa Jibril El yakub ne ya baiyana haka a zantawarsa da manema labarai a yola. Muakaddashin kwamishinan yace biyo bayan hada kai da sukayi da kungiyoyi shuwagabannin al umma harma da masu ruwa da tsaki domin fadakar da al umma musammanma wadanda sukayi rijistan katin zabe da su gaggauta zuwa ofishin hukumar dake kanaan hukumomi dake fadin jahar domin karban katin zabensu. A cewarsa dai hukumar ta INEC a fara bada katin zabe daga watan disemba wanda zata dakatar da bada katin a ranan 22-1-2023. Wasu daga cikin wadanda suka karbi katinsu sun baiyyanawa manema labarai yadda suka gamsu da yadda ake bada katin zaben duk dacewa ana samun kura kure domin wasu basuga katinsuba wanda aka shai

Rundunan yan sandan jahar Adamawa tana tsare da wasu matasa shida da ake zargin yan shilane

Image
Akokarinta na dakile aikata laifuka a fadin jahar rundunan yan sandan jahar Adamawa tayi nasaran cika hanu da wasu matasa yan shila guda shida wadanda suka addabi anguwar luggere kuma sun kware wajen balla shaguna da shiga gidaje. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a yola. Sanarwan ta cigaba da cewa biyo bayan da Jami an ta ke sintiri domin ganin ba asamu matsalaba a lokaci dama bayan ziyaran da shugaban kasa muhammadu Buhari zai kawo jahar Adamawa,Wanda hakan ya kai ga basu sa a kama wadanda ake zargin. A sanarwan anjiyo kwamishinan yan sandan jahar Adamawa Sikiru Kayode Akande ya yabawa Jami an yan sandan bisa na mijin kokari da sukayi wajen kama wadanda ake zargin. Kwamishin yan sandan ya kuma kirayi al umma dake fadain jahar da sukasance masu taimakawa rundunan yan sandan da wasu bayanai da zaibawa Jami an yan sandan damar kama masu aikata laifuka a

Zaben shekara ta 2023 an kirayi al ummah musulmai da suje su karbi katin zabensu.

Daga Sani Yarima Jalingo. Ganin cewa zaben shekara ta 2023 nata karatowa, an kara yin kira ga Al'umma dasu fita zuwa karban katinan zaben su a ofishoshin hukumar zabe ta kasa dake jahohin su. Wani Malamin Addinin Musulunci dake garin Mutum Biyu a karamar hukumar Gassol ta Jihar Taraba, Ustaz Sani Yusuf Darul-Hadith yayi wannan kiran alokacin da yake zantawa da wakilin mu dake Jalingo ta wayan hannu. Ustaz Sani Yusuf Darul-Hadith Mutum Biyu wanda muka zanta dashi ta wayan hannu jimkadan bayan an idar da sallan Juma'an data gabata yace nasihan da yayiwa al'umman musulmi a Babban masallacin kofar fadan mai Martaba Sarkin Mutum Biyu, Alh. Muhammadu Sani Duna shine na cewa karban katinan zaben su ya zama wajibi domin zai basu daman zaben 'yan takaran da suke da kyakkyawan zato a kansu. Ustaz Sani Yusuf Darul-Hadith Mutum Biyu ya kuma kara jawo hankalin matasa da karsu yarda arinka amfani dasu a matsayin 'yan barandan siyasa.

Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta kimtsa tsaf domin taran shugabann kasa Muhammadu Buhari.

Image
A kokarinta na inganta tsaro da kuma dakile aiyukan ta addanci rundunan yan sandan jahar Adamawa tace ta kimtsa tsaf domin daukan dukkanin mataken da suka dace domin ziyaran da shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kawo jahar Adamawa. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya baiyana haka a wata sanarwa da ya fitar a yola wanda aka rabawa manema labarai a yola. A sanarwan dai anjiyo kwamishinan yan sandan jahar Adamawa CP Sikiru Kayode Akande na cewa dukkanin shirye shirye ya kammala domin taran shugaban kasa do haka rundunan da sauran hukumomon tsaro sun hada kai domin ganin ba a samu matsalaba kafin dama bayan ziyaran shugaban kasa. Kwamishin yace za a takaita zirga zirgan ababen hawa a wuraren da shugaban kasa zaibi don haka al umma su kasance masu bin doka.

Gidan Rediyo Najeriya fombina fm yola ya jajintawa Uba Dan Arewa.

Image
Tawagan gidan Rediyon Najeriya Fombina FM yola sun kai ziyaran ta aziyar ga Uba Dan Arewa biyo bayan rasuwar mahaifins wato Alhaji Muhammed Dan malam Lau. Tawagan wanda Babban Manajan gidan Rediyo Najeriya fombina FM yola Alhaji Dahiru Garba Muhammed ya jagoranta. Inda yayi adu ar Alla madaukakin sarki ya jikansa ya kuma yi masa rahama yasa Aljannace makomansa. Yace a madadin gidan rediyo fombina yana mika ta aziyara ga iyalen marigayi inda ya baiyana rasuwar babban asarace baga iyalensa kawaiba harma da al ummah baki daya. Dayake jawabi a madadin iyalen marigayin wato Uba Dan Arewa ya nunu godiyarsa da jin dadinsa dangane da wannan ziyaran ta aziya wanda tawagan rediyo fombina suka kawo masa. Ya kuma yi adu ar Allah ma daukakin sarki ya bar zumunci tare dayin fatan Alheri ga ma aikata dama gidan resiyon baki daya. Alhaji Muhammed Dan Malam Lau dai ya rasune sakamokon gajeruwar rashin lafiya a cikin garin Lau dake jahar Taraba. Kuma ya rasu ya

Kungiyar yan sa kai ta karrama membobinta a jahar Taraba.

Image
Daga Sani Yarima Jalingo. Domin ganin ta inganta aiyukan jami anta kungiyar yan sa kai da aka fi sani vigilante ta shirya liyafa da baiwa kautar yabo wa wasu daga cikin yan kungiyar. Bikin liyafar da bada kautar yabonne a Jalingo fadar gwamanatin jahar Taraba inda yan kunguyar da yawansu ya kai dari da hamsin 150 suka karbi kautar yabon biyo bayan yanda suka sadaukar da kansu wajen gudanar da aiyukansu. Kwamandan kungiyar a jahar Taraba Bello Arabi da yake jawabi a wurin taron ya kirayi wadanda aka karramar da suci gaba da irin wannan na mijin kokari da sukeyi wajen kare al ummarsu. Kwamandan wanda mataimakinsa DCV Dominic Kabanya ya wakilta ya kirayi membobin kungiyar da su cigaba da baiwa hukumomin tsaro hadin kai domin kare rayuka dama dukiyoyin al ummah. a fadin jahar. Bello Arabi ya kirayi gwamnatin jahar Taraba dama kungiyoyi irinsu hukumar raya yankin arewa masau gabas NEDC da sauransu da aukasance suna taimakawa kungiyar tasu da ka

Alhaji Abubakar. Sadiq ya mayar da takardan tsayawa takaran shgabancin kungiyar SWAN ta kasa.

Image
Mataimakin shugaban kungiyar marubuta wasanni a Najeriya ta kasa SWAN Alh. Abubaoar Sadiq Mayoyo ya marayra da takardan da ya cike domin tsayawa takaran neman kujeran kungiyar. Da yake mikawa kwamitin shirya zaben kungiyar wanda Alhaji Abbas Shehu a k a Osculator ya kirayi sauran yan takaran da suyi amfani da damar da suke da shi na karaban takardan domin cikewa da kuma maryarwa. Yace a yanzu haka dai ga duk mai son tsayawa takaran mukamai dabab daban na kungiyar kofa a bude dake matukan abi dukkanin dokokon zaben da kwamitin ya gindaya. Shehu wanda yayi magana a madadin shugaban kwamitin Mr Sunday Agele ya tabbatarwa yan takaran cewa kwamitin ya kimtsa tsaf domin gudanar da zabe mai inganci. Da yake gabatar da taoardan a madadin Moyoyo shugaban kungiyar SWAN shiyar jahar Taraba Joachim Dangana Bandawa na TSBS ya membobin kungiyar a jahar Taraba da su marawa Abubakar Sadiq Moyoyo baya. Shugaban kungiyar a jahar Taraba yece tsayaw

Gwamna fintiri ya mika ta aziyarsa dangane da mutuwar Rodney Nathan.

Image
Gwamanan jahar Adamawa Ahmadu Umaru Fintin ya jajintawa shuwagabanin kungiyar malamai ta kasa N U T shipyard jahar Adamawa biyo bayan rasuwa shugaban kungiyar na jahar Adamawa kwamuret Rodney Nathan. Gwamnan ya mika ta aziyarsane a wata sanarwa daga sakataren watsa labarainsa Humwashi Wonosikou, inda inda ya baiyyana mutuwar Nathan a matsayin Babban rashine ga kungiyar ta N U T harma da Jahar Adamawa baki daya. Gwamnan ya kuma jajantawa Iyalen marigayin dama yan uwa da abokan arziki, gwamna fintiri ya baiyana marigayi a matsayin wanda ya taka rawan ganin wajen bunkasa ilimi tare da nuna kwazo a lokacin da yake gudanar da aiyukansa. Sanarwa ta ci gaba da cewa marigayi Rodney Nathan ya zama abun koyi ga rayuwarsa don kuwa ya bar babban gibi domin mutunne da ya da yake da muradun cigaban ilimi. Maragayi Rodney Nathan dai ya mutu a ranan talata sakamokon rashin lafiya da yayi fama da ita kuma ya mutune a Jos dake jahar filato. Kafin rasuwa

Mutane hudu ne suka mutu a wani hatsrin jirgi mai saukar angulu a Australia.

Image
Akalla mutane hudu ne suka gamu da ajalinsu sakamakon tsarin da wasu jirage masu saukan angulu sukayi a kusa da teku dake Australia. Jami an yansandan yankin da lamarin yaru sunce hatsrin ya farune alokacin da daya jirgin kekokarin tashi daya kuma yana sauka. Wadanda suka mutundai suna cikin jirgi dayane a yayinda sauran ukun kuma suna jinya cikin wani yanayi maiwahala. Cikin wadanda suka mutun dai biyu yan kasan ingilane karamar yadda mai magana da yawun ma aikatar kasashen wajen Australia ya baiyanawa manema labarai. Mutane biyar cikin shida wanda ke cikin daya jirgin da sukayi saukan gaggawa sun samu raunuka. Fira ministan kasa ta Australia Anthony Albanese yace kasar ta kadu kwarai da jin labarin aukuwar lamarin. Yace zasu dauki dukkanin matake da suka dace domin kula da wadanda suka jikkata sakamakon tsarin.

Ankirayi mawallafa labarai ta yanan gizo da suyi amfani da kwarewasu wajen bada ingantattun labarai.

Image
An kirayi mawallafa labarai ta nan gizo da sukasance masuyin amfani da kwarewarsu wajen yada labarai domin Samun cigaban zaman lafiya. Kiran na zuwane a taron da kungiyar mawallafa labaria ta yanan gizo na yankin arewa kasau gabas wato NOMAS ta gudanar a yola. Taron wanda Muhammed Adamau dodo ya jagoranta inda aka tattauna batutuwa da dama da zumar come gaban kungyar ciki harda shawartar yan kungiyar da suyi rijista da uwar kungiyar yan jarida ta kasa wato NUJ dama hukumomin tsaro domin inganta aiyukasu yadda yakamata. An kuma kirayi yan kungiyar da su maida hankali wajen bin ka idodin aikin jarida tare da gudanar da aiyukan yada labarai da zai ilimantar da nishadantar da al ummah. Kuma su kasance masu gudanar da aiyukansu bisa kwarewa wanda hakan zai taimaka wajen cigaban kungiyar yadda yakamata. A karshe an bukaci yayan kungiyar su maida hankali wajen bada rahotani da zasu kawo hadin kai dama zaman lafiya a tsakanin al ummah baki day

Gidaje hudu da shaguna sha daya ne aka kona a wani rikicin kabilanci a karamar hukumar lamurde dake jahar Adamawa.

Image
A kalla gidaje hudu tare da shaguna sha daya aka kona biyo bayan sabon rikicin kabilanci da ya barke a karamar hukumar Lamurde dake jahar Adamawa. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SPSuleiman Yahaya Nguroje ya tabbatarwa Jaridar Al Nur akuwar lamarin inda yace rikicin dai ya farune a tsanin kabilar waja da lunguda kawo yanzuma ana cigaba da gudanan da bincike domin gano musabbabin tashin rikicin da kuma gano wadanda ke da hanu a cikin rikicin. So Suleiman yace da jin labarin tashin rikicin hakan yasa kwamishinan yan sandan jahar Adamawa CP Sikiru Kayode Akande baiyi kasa a gwiwaba wajen tura Jami an yan sanda zuwa wurin da lamarin ya faru domin kwantar da rikicin. Suleiman Yahaya yace an tattauna da masu ruwa da tsaki da suka hada birget kwamanda na sojoji shuwagabanin kananan hukumomin Lamurde da Guyuk da sarakunan gargajiyan yankin harma da matasa a wani mataki na kwantar da rikicin baki daya. A yanzu haka dai kura ta lafiya biyo bayan tura Jami

Kugiyar Malamain Jami o i a Najeriya ASUU tace karin kudin makarta da hwamnati tayi baizo mata da mamakiba.

Image
Kungiyar malamai Jami o i a Najeriya wato ASUU shiyar Jami ar Modibbo Adama dake yola tace daman abunda suke gudu kenan na kada gwaknati ta kara kudin makaranta amma sai aka kasa fahintarsu harma da zargin cewa suna wannan fafutuka ne domin Kansu. Shugaban kungiyar Malamain Jami o i na Jami ar Kodibbo Adama Dr El Maude Jibril Gambo na ya bayana haka a zantawarsa da Jaridar Al Nur a yola. Dr El Maude yace sukam karin kudin baizo musu da mamakiba saboda daman suna fadawa mutane musammanma iyaye da su maramusu baya a kokari da sukeyi na ganin an inganta Jami o in kasan nan amma suka ki wasuma suka shiga zarkinsu da lalata bangaren ilimi. Dr Jibril yace yanzu kam yar manuniya ta nuna cewa ashe abunda kungiyar keyi yana kan hanya saboda haka ya kamata suyi karatun ta nutsu sukarayi gwamnati da ta rage kudin makarantar saboda yaran talakawa su samu suyi karatu yadda ya kamata. Yace ko shakka babu hwaknati tana iya daukan nauyin kakarantu ba tare da Ka

An kirayi yan jarida da su sanya tsoron Allah a zukatansu a duk lokacinda suke gudanar da aiyukansu.

Image
Daga Sani Yarima Jalingo. An jawo hankalin Yan Jarida da suji tsoron Allah wajen kaucewa bada labarin da zai kawo tashin hankali a kasa, musamman a wannan lokacin da zabuka ke karatowa a wannan shekaran. Tsonhon Mukaddashin Gwamnan Jihar Taraba, Sanata Sani Abubakar Danladi yayi wannan kiran alokacin da yake amsa tambayoyin daga manema labarai a garin Jalingo.fadar gwamaatin jahar Taraba. Tsonhon Mukaddashin Gwamnan kuma tsonhon Sanata, Malam Sani Abubakar Danladi yace idan har Yan Jarida zasu tsaya kan gaskiya wajen bada labarai yadda suke, toh babu shakka za'a samu. zaman lafiya a Jihar dama kasar Najeriya baki daya. "Yanzu zan jawo hankalin Kun tunda kuka yimini wannan tambayan kace abinda baku iya tambaya in bada amsa toh kuma zan bada amsa, don Allah ku tsaya tsakanin ku da Allah ku bada rahoton abinda kuka san bazai tada hankalin kasa ba. "Domin yawaci matsaloli kashi chasa'in da Tara (99%) daga wurin ku yake fitowa, ab

Rundunan yan sandan jahar Adamawa tasha alwashin ganin an gudanar zaben 2023 lafiya,

Image
Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta lashi takwabin ganin an gudanar da Babban zaben shekara ta dubu biyu da ashirin da uku cikin kwanciyar hankali ba tare daatsaloliba. Rundunan ta baiyana haka ne a wata sanarwa da kakakin rundunan yan sandan na jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ya sanyawa hanu wanda aka rabawa manema labarai a yola. Rundunan tace ta dauki dukkanin matakai da suka dace domin ganin ba a samu tashin hankaliba a lokaci dama bayan zaben.wanda kuma daukan matakin hakan ya biyo bayan tattaunawa da kwishinan yan sandan jahar Adamawa Sikiru Kayode Akande yayi da dukkanin masu ruwa da tsaki dangane da tsaro domin ganin ba a samu matsalaba a lokacin zabe. Kwamishinan ya kuma shawarci sauran hukumomin tsaro da suyi aiki kafada da kafada domin ganin an samu nasaran gudanar da Babban zaben. Tare da kiran Jami an tsaro da sukasance masu sanya ido sosai domin kama duk wanda yayiwa doka karan tsaye. Kwamishinan ya kuma tabbatarwa al umma ja

An kirayi mazauna gundumar Nasarawo Abba da sukasance masu hada kansu.

Image
An kirayi mazauna gundumar Nasarawo Abba dake cikin karamar hukumar yola ta arewa a jahar Adamawa da su kasance masu hada kansu a koda yaushe domin samun cigaban gundumar harma da samar da zaman lafiya a gundumar baki daya. Hakimin Nasarawa Abba kuma sarkin sudan Adamawa Alhaji Abubakar Aliyu Mustafa ne yayi wannan kira a lokacinda yake jawabi a dai dai lokacinda wadanda suka samu sarautun gargajiya a gundumar na Nasarawo Abba suka kaimasa ziyaran godiya a fadarsa dake Nasarawo Abba. Hakimin yace hadin kai a tsakanin al umma abune da yake da mutukam muhimkanci don haka akwai buktan al umma su kasance masu yin dukkanin abunda suka dace domin hadin kai dama cigaba. Alhaji Abubakar Aliyu Mustafa ya shawarci al umma gundumar ta Nasarawo Abba da su bashi hadin kai da goyon baya domin ganin an wanzar da zaman lafiya dama cigaban gundumar baki daya. Ya kirayi wadanda suka samu mikamen masarautun gargajiya da su gydanar da aiyukansu bilhakki da gaskiya da