Posts

Showing posts from September, 2023

An shawarci Al umma da bunkasa harkokin Al adu domin Samar da hadin Kai a tsakanin Al umma.

Image
. An shawarci al umma da su maida hankali wajen kula dama bunkasa harkokin al adu domin samun hadin kai harma da wanzar da zaman lafiya a tsakanin Jama a. Shugaban kungiya baoys brigade a Najeriya shiyar karamar hukumar Girei a jahar Adamawa Mr Joshua Philemon ne ya bada wannan ahawara alokacinda yake jawabi a wurin bikin rawai rawain gargajiya da kungiyar ta shirya a Karamar hukumar ta Gieri a jahar Adamawa. Mr Joshua Philemon yace makasudin shirya wannan biki shine domin musayar fasaha da da a a tsakanin membobin kungiyar ta Boys brigade da kuma samun damar koyon Al adu daban daban domin samar da cigaba yadda ya kamata. Ya kuma jaddada cewa koyon Al adu daga Al ummomi daban daban zai takarawan gani wajen kare Al adu dama infanta rayuwar Al umma baki daya. Ya kuma kirayi membobin kungiyar da sukasance masu bin doka da oda a koda yaushe domin samar da inganceccen tsaro harma da cigaba. A jawabinsa uban kungiyar ta boys brig

Akalla mata hamsine wadanda ke dauke da cutar yoyo fitsarin akayiwa fida kyauta a jahar Gombe.

Image
Daga Ibrahim Abubakar Gombe An kirayi magidanta da sukasance suna baiwa iyalen su kula na musamman a lokacinda suke dauke da juna biyu domin kaucewa kamuwa da cutar yoyon Fitsari wato VVF. Shugaban kungiyar dake yaki da cutar yoyon fitsari wato Gidauniyar Fistula a Najeriya (FFN) malam Musa Isa ne yabaiyana haka a lokacinda ya jagoranci yiwa mata dake dauke da cutar yoyon fitsarin kyauta a jahar Gombe. Gidauniyar ta fistula tare da hadin gwiwar asusun jama a na majalisar dinkin duniya UNFPA da kuma NORWEGIAN GOVERNMENT sunyiwa mata akalla hamsin fidar cutar yoyon fitsari kyauta wandama tunin aka sallamesu daga aaibitin dake jahar Gombe. Matan wadanda suka fito daga sassa daban daban dake fadin jahar. Kuma an daukai matakin taimaka musu ne duba da irin wahalar rayuwa da suka tsnci kanau a ciki biyo bayan kamuwa da cutar na yoyon fitsari. Dr Sa ad Idris she nema ya jagiranci l

Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta tarwatsa tare kama wadanda ake zargi dayin garkuwa da mutane domin Neman kudin fansa.

Image
kokarinta na inganta tsaro da Kuma jaddada aniyarta na dakile aiyukan ta addanci a tsakanin Al umma. Rundunan yan sandan jahar Adamawa tare da hadin gwiwar mafarauta da kungiyar miyetti Allah sun dakile aiyukan masu garkuwa da mutane da suka addabi yankin Tambo a karamar hukumar Girei a jahar Adamawa. Kawo yanzu dai Rundunan yan sandan na tsare da mutane bakwai wadanda ake zargi da aikata laifuka garkuwa da mutane a yankin na Tambo. An samu nasaran cika hanu da mutane biyo bayan samun bayanain sirri da Kuma dabaru da aka dauka Wanda hakan yasa suka yarwatsa wadanda ake zargi daga maboyarsu biyo bayan garkuwa da sukayi da wani Mai suna Koire Alhaji Ruwa inda suka bukaci kudin fansa da yakai nera milyon goma. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar a yola. Sanarwa ta baiyana cewa kwamishinan yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola ya

Rundunan yan sanda a jahar Adamawa ta kama wani da ake zargi dayiwa yar shekaru fyade.

Image
Rundunan yan sanda a jahar Adamawa tayi nasaran cafke wani da ake zargi da yiwa wata yarinya yar shekaru hudu da haifuwa fyade. Kakakin rundunan yan sandan a jahar Adamawa SP Suleiman Yahay Ngurojene ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a yola. Sanarwan tace mutumin da ake zargi mai shekaru talatin da biyu da haifuwa wato Mika Bitrus wanda yake zaune a Garin Sangere kan titin zuwa Girei wanda kuma ana zarginsa da yuwa wata yarinya mai shekaru hudu da haifuwa fyade. An dai samu nasaran damke mutuminne biyo bayan karafi da uwar yarinyar Fatsuma Abdullahi da shigar a ofishin yan sanda dake Girei, wanda kuma hakan yasa rundunan yan sandan batayi kasa agwiwaba wajen gudanar da bincike akan lamarin. Bincike da aka gudanar ya baiyana cewa shi wanda ake zargin dai masana ar kafintane kuma ya aikata laifinne ga yar makwabcinsa. Tunin dai kwamishinan yan sandan jahar Adamawa Afolabi Ba

Tashin bom yayi sanadiyar kashe mutane 50 a Pakistan.

Image
. Akalla mutane hamsin suka mutu wasu hamsin kuma suka jikkata sakamokon harin kunan bakin wake da aka kai a wurin bikin Maulidi a Pakistan kamar yadda hukumar Yan sandan kasar ta baiyana. Lamarin dai ya farune a kusa da masallaci dake arewa masau yamma na lardin Balochistan a dai dai lokacinda ake gudanar da bikin Maulidi tunawa da ranan haifuwar mazon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi. Yanzu haka dai hukumomi a lardin na Balochistan sun aiyana dokan ta baci domin maida da zaman lafiya a yankin. Kawo yanzu dai ba wata kungiya da ta dauki nauyin Kai harin. An sake samun tashin wani bom a masallaci dake kusa da birnin Peshawar a Khyber dake lardin Pakhtunkhwa. Sai dai har yazuwa yanzu ba Akai ga gano wadanda suka jikkata ko rasa ratukaba. Duk da cewa bom din yayi sanadiyar lalata gine ginen masallacin.

Rundunan yan sandan Najeriya zata gudanarwar karnuka Alura riga kafi kyauta a fadin Najeriya

Image
A yayinda aka gudanar da bikin ranan cizon Kare na duniya rundunan yan sandan Najeriya ta ta kudiri aniyar yiwa karnuka aluran riga kafi domin rage kaifin guba a wani mataki na inganta kiwon lafiya a tsakanin al umma. Kakakin rundunan ACP Olumuyiwa Adejobi ne ya baiyana haka a wata sanarwa ya fita aka rabawa manema labarai a Abuja. A sanarwan anjiyo Babban sifeton yan sandan Najeriya Kayode Adeolu Egbetokun na cewa bikin ranan cizon kare karo na sha bakwai mai taken lafiya ga kowa don haka rundunan ta dauki dawainiyar yiwa karnuka aluran Riga kafi kyauta, a duk fadin Najeriya. A wani mataki na kawar da cutar dake sahafa mutane dama dabbobi. Don haka rundunan yan sandan a Najeriya taga ya dace ta dauki matakin magance matsalar na cizon karnuka a tsakanin al umma , don haka daga yau 28-9-2023 za a fara aluran Riga kafin a dukkanin karnuka a dukkani cibiyoyin kula da lafiyar dabbobi na rundu

An shawarci manoma da sukasance suna tuntuban malamain goma domin bunkasa harkokin noma.

Image
An shawarci manoma da sukasance masu neman ilimin harkokin noma a koda yaushe domin samun damar gudanar da inganceccen noma harma da samar da wadaceccen abinci a fadin Najeriya baki daya. Alhaji Adamu Jnigi ne ya bada wannan shawara a zantawarsa da jaridar Al Nur Hausa a yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Alhaji Adamu Jingi yace yanzu haka noma ya koma na zamani don haka akwai bukatar manoma su maida hankali wajen tuntubar malamai gona domin kaucewa da na sani. Kuma da zaran sunga abunda basu ganeba a gonakainsu da su gaggauta nemo malamain gona domin magance matsalar. Da yake amsa tabbaya dangane da mutane su shiga harkokin noma sai Alhaji Adamu yace yakamata Jama a su rungumi harkokin noma, domin a cewarsa Najeriya tana da sama da mutane milyon biyu kuma mutane kadanne suke noma. Don haka akwai bukatar karin jama a da su shiga a dama dasu a harkokin noma wand

Gobara tayi sanadiyar mutuwar mutane dari a wurin bikin daurin aure a Iraki.

Image
Akalla mutane dari ne suka gamu da ajalinsu sakamokon daahin gobara a wurin bikin aure a yayinda mutane dari da hamsin suka jikkata a yankin arewacin Iraki. Daruruwan mutane ne dai suna gudanar da bikin aure a garin Al Hamdaniya dake arewacin kasar Iraki kwatsam sai gobara ta tashi a wurin bikin. Kawo yanzu dai ba asan dalilin tashin wutaraba . Gobaran tayi sanadiyar lalata waau sassan gine gine da ake gudanar da bikin aure. Sai dai ba a tabbatar ko lamarin ya ritsa da amarya ko Angoba duka da cewa wasu rahotannin na cewa amaryar da ango suna cikin wadanda suka mutu.kamara yadda kafafen yada labarai kasar ta Iraki suka baiyana. An dai kai watanda suka jikkata zuwa Asibiti domin yi musu jinya.

Rundunan yan sandan jahar Adamawa tana tsare da wani matashi da ake zargi da kisan Kai.

Image
A yanzu haka rundunan rundunan yan sandan jahar Adamawa tana tsare da wani mataahi mai suna Zakaryau Sa ad dan shekarau 19 da haifuwa wanda ke zaune a Anguwar Wuro Hausa dake cikin karamar hukumar Yola ta Kudu dake jahar Adamawa bisa zarginsa da kashe wani matashi mai suna Muhammed Yahaya. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da rabawa manema labarai a yola. Kama wanda ake zargin biyo bayan rahoton da mazauna Anguwar Damdu a karamar hukumar yola ta kudu suka kai ofishin yan sanda cewa gawani da basusan ko wayeba kwance a cikin jin biyo bayan jimasa da akayi a wuya. Nan dana DPO ofishin yan sandan dake yola ya garzaya dashi zuwa asibitin daga bisani ya mutu. Tunin kwamishina yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola ya umurci mataimakin kwamishinan yan sanda dake kula da sashin binciken manyan laifuka wato CID da yacigaba da gudanar bincike dangane da

Gwamnatin jahar Adamawa ta lashi takwabin inganta harkokin noma a fadin jahar.

Image
Gwamnatin jahar Adamawa ta kudiri aniyar inganta harkokin noma dama samar da kasuwancin kayakin noma a fadin jahar baki daya. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jahar Adamawa ne ya baiyana haka a lokacinda yake jawabi a wurin kaddamar da bada rance kasuwamcin kayakin noma karkashin shirin nan na Agribusiness. Wato Adamawa Agribusiness Support ADAS Programme.wanda ya gudana a gidan gwamnati dake nan yola. Gwamna Fintiri yace shirin zaitaimakawa wadanda zasu amfana da tsarin ta samun damar basu rance daga Bankuna domin gudanar da harkokinsu yadda ya kamata. Gwamna ya kuma kirayi daukacin al umma jahar da sucigaba da hakuri biyo bayan hawhawan farashin kayakin abinci dama tsadar rayuwa da ake ciki da yardan Allah nan bada dadewaba komai zai koma daidai. Ya kara da cewa gwamnatinsa za

Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta lashi takwabin Saka kafar wando Daya da duk Wanda yayiwa doka Karen tsaye a lokaci dama bayan bukukuwar Maulidi.

Image
Rudunan yan sandan jahar Adamawa tare da sauran hukumomim tsaro sun kimtsa tsaf domin ganin an gudanar da bukukuwar Maulidi lafaiya ba tare da matsalaba. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar a yola wanda aka rarrabawa manema labarai. Sanarwa na mai gargadin cewa rundunan zata saka kafarwando daya ga duk wanda ke barazanar karya doka ko kuma ko kuma yiwa zaman lafiya barazana. Don haka jama a su kaucewa duk abinda zai kawo tashin hankali a lokaci dama bayan bukukuwar bikin na Maulidi a fadin jahar. Sanarwan ta cigaba da cewa Al umma musulmai su tafi zuwa wuraren da za a gudanar da bukukuwar lafiya ba tare da fargababa domin rundunan yan sandan ta dauki dukkanin matakai da suka dace domin kare rayuka dama dukiyoyin Jama a. Sanarwa ta kirayi daukacin al umma da su baiwa hukumomin tsaro hadin kai da goyon baya da kuma kai raho

Kotu sauraren kararrakin zabe gwamna ta tabbatarwa gwamnan jahar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya cewa shine halacceccen zaben gwamnan jahar Gombe.

Image
Rahitanni daga jahar Gombe na cewa kotun sauraren koke koken kararrakin zabe tayi watsi da kaararakin da aka shigar mata na kalubalantar nasaran cin zaben gwamnan jahar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya da mataimakinsa Manasah Daniel Jatau. Kotun ta babbatarwa gwamnan cewa shine halalceccen gwamna a zaben gwamna da akayi a shekara ta dubu biyu da aahirin da uku a jahar ta Gombe. Kotun mai mutum uku karkashin jagorancin mai shariya S B Belgore tayi watsi da karanda yan takaran gwamna a karkashin jam iyar ADC Nafi u Bala dana jam iyar PDP Jibril Barde inda suke kalubalantar nasaran cin zabe da gwamna Inuwa Yahaya yayi da shi da mataimakinsa Manasah Daniel Jatau. A karanda jam iyar PDP ta shigar tare da dan takaranta inda suka zargi cewa an tafka magudi a zaben wanda hakan ya suka garzaya kotu domin bin kadun zaben. Itama anata bangaren Jam iyar ADC da dan takaranta suma kalubalantar zaben sukayi da cewa an tafka ar

Gwamnatin jahar Gombe ta dauki dawainiyar Kai daluben jahar zuwa jihohin da suke karatu karkashin Shirin misayan dalube.

Image
kokarinta na magance matsin tattalin arziki da aka shiga sakamokon cire tallafin mai fetur gwamnatin jahar Gombe ta dauki dawainiyar kai daluben jahar dake karatu a makarantu daban daban dake fadin arewacin Najeriya. A cikin tsarin nan na musayar daluben. Da yake yiwa dalube jawabi kafin tashinsu zuwa jihohi da suke karatu darctan shirin na musayan dalube na ma aikatan ilimi a jahar Gombe Audu Garba ya shawarci daluben da sukasance masu nuna halaye na gari a duk inda suke karatu domin samun albarka da kuma cigaban ilimi da suka koya. Ana shirya tsarin musayan daluben ne domin samar da hadin kai a tsakanin daluben dake yankin na arewacin Najeriya. Audu Garba ya yabawa gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na jahar Gombe bisa daukan dawainiyar kai daluben a jihohi daban daban dake yankin arewacin Najeriya. Darectan ya baiyana cewa an dauki matakin hakane domin sauwakawa iyayen daluben duba da irin yanayi

An shawarci Al umma musulmai da suyi amfani da wannan lokaci na bukukuwar Maulidi wajen yiwa kasa Adu a.

Image
yayinda ake cigaba da bukukuwar maulidi domin tunawa da ranan haifuwar mazon Allah tsira da amincin Allah su tabbatar agareshi. An shawarci malamai masu gudanar da jawabai dama nasihohi a wuraren bukukuwan bikin na maulidi da su maida hankali wajen yin dukkanin abinda zai kawo hadin kai da zaman lafiya a tsakanin Al umma. Shugaban Annahada International Islamic Organization shiyar jahar Adamawa Sheik Modibbo Aliyu Wuro Yobbe ne yayi wannan kira a zantawarsa da manema labarai a Yola. Sheik Modibbo yace ana gudanar da bukukuwar maulidinne domin tunatar da Al umma musulmai halayen manzon Allah da Kuma tarihinsa dangane da rayuwarsa da Kuma yadda ya zauna da jama a daban daban. Don haka ya kamata Al umma musulmai suyi koyi da halayen manzon Allah a Koda yaushe domin ganin an samu zaman lafiya a tsakanin Al umma. Modibbo Aliyu ya Kuma ja hankalin mahalarta bukukuwar Maulidi da sukasance suna amfani da abimda

Gwamna Ahmadu Fintiri na jahar Adamawa ya sha alwashin bunkasa harkokin kwallon dawaki wato polo a fadin jahar.

Image
Gwamnatin jahar Adamawa ta baiyana shirin ta na shiga ƙawance da kungiyar wasan kwallon dawaki ta kasa domin bada karfin gwiwar shiga harkokin wasar a jahar. Gwamnan jahar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri ne ya sanar da haka yayin bikin rufe gasar kwallon dawaki na 2023, wanda kungiyar ya shirya a birnin Yola fadar jahar. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri yace gwamnatin jahar za ta ci gaba da tallafawa wasar a jahar domin cin gajiyar albarkatun da ke cikin ta. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri wanda ya baiyana sha'awar shi a wasan yace wasan na kunshe da harkokin bude ido da na tattalin arziki, tare da karin cewa gwamnati zata tabbatar da kyakkyawar yanayi da zai kawo ci gaban wasan. Gwamnan yace, kasancewar jahar Adamawa wata muhimmiyar matattarar na yankin arewa maso gabashin Najeriya, jahar na shirye domin shiga ƙawance dama tallafawa kungiyar wasan ƙwallon dawaki ta kasa domin tatsar d

An karrama kawamishinan Yan sandan jahar Adamawa da wasu Jami ai biyu.

Image
An yabawa rundunan yan sandan jahar Adamawa bisa kokarinta na inganta tsaro dama kare rayuka da dukiyoyin Al umma baki daya. Shugaban kungiyar Daliben Arewacin Najeriya wato GAMJI kwamuret Umar D Afkawa ne yayi wannan yabao a lakacinda yake jawabi a wurin bikik karrama kwamishinan yan sanda da PPRO da kwamandan Crack wanda ya gudana a ofishin kwamishinan yan sandan dake ahelkwatar rundunan daka yola. Kwamuret Umar D Afkawa yace rundunan karkashin jagorancin kwamishinan yan sandan a jahar Adamawa Afolabi Babatola ya taka rawan ganin wajen samar da tsaro mai inganci a tsakanin jama a musammanma daukan matakai da yakeyi akan masu aikata lafuka daban daban da suka hada da fashi da makami, shila, garkuwa da mutane da dai sauransu. Kwamishinan ya taka rawan ganin wajen gudanar aiyukan da zaikawao zaman lafiya a tsakanin al umma don hakanema kungiyar daluben t

An shawarci malamai masu gabatar da nasihohi a wurin bukukuwar maulidi da su maida hankalin wajen hadin kan Al umma.

Image
An kirayi malamai musammanma wadanda ke gabatar da nasihohi da jawabai a wurin bukukuwar maulidi da su maida hankali wajen fadakar da al umma musulmai dangane da hadin kai dama tarbiya a tsakanin al umma. Mallam Isma ila Modibbo Umar ne ya baiyana haka a zantawarsa da jaridar Al Nur Hausa a yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Malam Isma ila Modibbo yace yana da muhimmanci malamai su maids hankali wajen baiyana halayen manzon Allah yadda ya zauna da kowa lafiya da kuma jan hankali jama a wajen yin karatu domin samun cigaban addinin musulunci. Malam Isma ila yace bikin maulidi yana da tarihi sosai saboda haka ana gudanar da bikinne domin tunawa da ranan haifuwar manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi. Tare kuma da gudanar da nasihohi daban daban dama baiyana tarihin manzon Allah. Malam Umar ya kuma kara da cewa akwai bukatar Al umma musulmai sukasance masuyin koyi da halayen manzon Allah. Wanda acewarsa hakan zaitai

Kamfanin Auwalus Business Concept ya dauki matasa aiki a wani mataki na rage rashin aikinyi a tsakanin matasa.

Image
Kamfanin Auwakus Business Concept ya fara harar da ma aikata da ya dauka aiki domin ganin sun gudanar da aiyukansu yadda ya kamata ba tare da matsalaba. Shugaban kamfanin Alhaji Auwal Usman ne ya baiyana haka a lokacinda ya jagorancin horar da ma aikata a kamfanin dake yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Alhaji Auwal yace sun dauki matakin horar da ma aikatanne domin sanin makaman aiki ganin cewa basu samu matsalar gudanar da aiyukansuba. Ya kuma jaddada aniyarsa na ganin cewa matasa sun dogara da kansu wajen samun sana o i daban daban wanda acewarsa hakan zai taimaka wajen inganta rayuwar matasan harma da samar da zaman lafiya a tsakanin jama a baki daya. Da wannan nema yake shawartan matasa da kada suyi kasa a gwiwa wajen rungumar sana o i dogaro da kai domin kare nartabarsu dama cigaban al umma.

Ofishin Jakadancin Amurka a Najeriya ya fara horar da mata yan Jarida na kwanaki uku a jahar Taraba.

Image
Daga Ibrahim Abubakar Jalingo Ofishin jakadancin Amurka dake Najeriya ya fara horar da mata yan Jarida na kwanaki uku a jahar Taraba domin inganta aiyukansu a zamunance ba tare da fargaba ba da Kuma bada rahoton da zai kawo cigaba a yankin arewa masau gabas. Horan wanda ofishin jakadancin Amurka tare da hadin gwiwar kungiyar na Organization for Innovation anda Sustainable Development suka shirya a wani matakin na Samar da dai daito aikin Jarida ga mata a yakin na arewa masau gabashin Najeriya. Yan Jarida mata a jahar Taraba dai na fuskantar kalubale da dama a duk lokacinda suke gudanar da aiyukansu a Arewacin Najeriya. Wani masana dai na cewa horon zai karwa matan kwarin gwiwar gudanar da aiyukansu bisa kwarewa domin ganin an samu nasaran cigaban dama wanzar da zaman lafiya a yankin na arewa masau gabas dama kasa baki Daya.

An kirayi mata da sukasance masu shiga harkokin siyasa domin damawa dasu a cikin harkokin gwamnati.

Image
An shawarci mata da sukasance masu shiga a dama dasu a cikin harkokin siyasa domin samun kyakkawar gwamnati dama adalci a tsakanin al umma. Dr Erisa Danladi ce ta baiyana haka a wajen taron kwana daya wanda cibiyar musayar bayanai da cigaban al umma wato DEC ta shirya a jahar Gombe. Dr Erisa wanda itacema bakuwa mai jawabi a wurin taron ta baiyana cewa abinda yake hana mata shiga siyasa domin adama dasu sun hada da rashin kudi, matsalar hangar siyasa da dai sauransu. Tace yana da muhimmanci in aka samu mata suna rike da mukamai daban daban ta kara dacewa in har gwamnatoci a dukkanin matakai zasu baiwa mata kaso talatin da biyar na guraben aiki dama mukamai kamar yadda kotu ta bayar matan zasu samu nasaran samun wakilci a cikin harkokin gwannati. Ta kuma baiyana cewa yana da muhimmanci a shirya gangamin wayar da kai domin samar da doka da zaibai

Kwamishinan Yan sanda jahar Adamawa ya rarraba kayakin tallafi.

Image
Kwamishinan yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola ya rarrabawa Jami an yan sanda kayakin tallafi wanda gwamnatin jahar Adamawa ta bayar. Hakan na kunshene a cikin wata sanarwa dauke da snaya hanun kakakin rundunan yan sanda jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje da ya fitar a yola. Kwamishinan yan sandan ya karbi buhunan shinkafa dari da hamsin (150) an kuma rarrabawa marassa karfin dake cikin Jami an yan sandan, musammanma marayu wadanda iyayensu suka rasa rayukansu a lokacinda sukeyiwa kasa aiki. Kwamishinan yan sandan ya godewa gwamnatin jahar Adamawa bisa kokarinta na cigaba da taimakawa rundunan yan sandan don haka rundunan zata cigaba da inganta tsaro domin kare rayuka dama dukiyoyin al umma jahar baki daya.

Rundunan yan sandan jahar Adamawa yanzu haka tana tsare da wani Wanda ake zargi dayiwa matar makwabcinsa fyade

Image
yan sandan a jahar Adamawa tayi nasaran cafke wani dan shekaru talatin da shida da haihuwa wanda ke zaune a Anguwar Diocese a Kala a dake cikin karamar hukumar Hong bisa zarginsa dayiwa matar bakabcinsa yar shekara ashirin da daya fyade. Jami in hulda da jama a na rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar wanda aka rabawa manema labarai a yola. Sanarwan tace mutumin mai suna Jafar Adamu ya samu nasaran yin hakane bayan ya fahinci makabcin nasa baya gida ya tafi gona saboda haka ya kutsa cikin gidan tare da tilasawa matar makabcin nasa da ta amince da bukatar tashi ko kuma ya jimata. Bincike ya nuna cewa wanda ake zargin ya shiga gidanne fuskarsa a rufe dauke da wuka inda ya tilasta mata da ta yarda da bukatarsa, sai akayu rashin sa a yana cikin aikata laifin sai abinda yasa a fuskarsa ya fadi dagan ne fa yayi tsalle da taga ya fi

Rundunan yan sanda a jahar Adamawa ta cika hanu da wani da ake zargi da yiwa wata daluba fyade.

Image
Rundunan yan sanda a jahar Adamawa tace tayi nasaran cafke Dan shekara ashirin da uku Mai suna Safiyanu Abubakar dake zaune a Unguwar chamber a cikin karamar hukumar Toungo a jahar Adamawa bisa zarginsa da yiwa wata daluba fyade. Wanda ake zargin dai yayi anfani damar ne a yayinda ya ziyarci daluba inda yayi anfani da wani sanadari ta sanya mata a cikin abinsha domin ya gusar mata da hankali. Wanda ake zargi ya tabbatar da aikata laifi inda yace yayi anfani da wannan damarne wajen sanya mata abinda zai gusar mata da hankali. Tunin dai kwamishinan Yan sanda jahar Adamawa ya bada umurnin gudanar da bincike kan lamarin Kuma da zaran an kammala bincike za a gurfanar da Wanda ake zargin gaban kotu domin ya fuskanci shariya.

An nada gwamnan Babban Banking Najeriya wato CBN.

Image
shugaban kasa Bola Tinubu ya nada OlaYemi Cardoso a matsayin gwamnan Babban Bankin Najeriya wato CBN. Hakan na kunshene a cikin wata sanarwa dauke da sanya hanun. Mai magana da fadar shugaban kasa Ajuri Ngelale Wanda ya fitar a Jumma a nan. nadin na zuwane bayan dakatar da Emefiele daga mikamin gwamnan Babban Bankin.

An kirayi kungiyoyi da gwamnatoci dasu maida hankali wajen aiyukan jinkai.

Image
An kirayi gwamnatoci da kungiyoyi masu zaman kansu da su maida hankali wajen aiyukan jinkai domin taimakawa marassa galihu dama yan gudun hijira a fadin kasa baki daya. Mataimakin shugaban kungiyar agaji na Jama atul Nasaril Islam na kasa, kuma shugaban kungiya a jahar Adamawa kana short gaban majalisar addinin musulunci a jahar Adamawa Alhaji Gambo Jika ne yayi wannan kira alokacinda yakeyiwa manema labarai jawabi dangane da ranan agaji ta majakisar dinkin duniya a yola. Alhaji Gambo Jika yace kungiyar agaji na Jamatu Nasaril Islam ta dade tana taimakawa a bangarori daban daban da zaran bukatar haka ta taso. Wanda hakan yasa kungiyar ta fadada aiyukanta zuwa dukkanin kanana hukumomi aahirin da daya dake fadin jahar Adamawa. Alhaji Gambo yace don haka yakanata ace masu hanu da shuni dama gwamnatoci dama kungiyoyi masu zaman kansu su dukufa wajen gudanar da aiyukan agaji domin ganin an samu walwala atsakanin

Rundunan yan sandan Najeriya ta bugi kirjin inganta tsaro a fadin kasa baki Daya.

Image
yan sandan Najeriya tasha alwashin inganta tsaro a fadin kasar domin dakile aiyukan ta addanci a wani mataki na maido da zaman lafiya a dukkanin sassan Najeriya. Babban aifeton yan sandan Najeriya Kayode Adeolu Edbetokun ne ya baiyana haka a lokcinda ya jagoranci wani taro da rundunan ta gudanar da manyan Jami an yan sandan da suka hada mataimakan Babban sifeton yan sandan, da kwamishinoni, dama kwamandodi daban daban dangane da mataki da ya kamata a dauka domin magance matsalar tsaro da ake fama dashi. A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunan yan sandan na kasa ACP Olumuyiwa Adejobi ya fitar ta baiyana cewa taron ya hada dukkanin masu ruwa da tsaki domin tattaunawa da kima zakulo hanyoyin samun nasaran takawa ta addanci birki. Da yake jawabi dangane da zaben gwamnonin jihohin Bayelsa, Imo, Kogi, dake tafe yace an dauki dukkanin matakai da suka dace domin ganin an samu nasaran gudanar da zaben cikin tsanaki

Majalisar wakilai kasar Amurka zata fara bincike domin tsige Joe Biden.

Image
Majalisar wakilain kasar Amurka tace zata gudanar da bincike kan shugaban kasa Joe Biden domin lalubo hujjojin tsigeahi daga kan Mulki. Kakakin majalisar Kevin McCarthy ne ya sanar da haka inda yace bincike zai duba zargi da ake masa na yin anfani da Iko, harma da cin hanci da rashawa. Na umurci kwamitin da aka kafa dangane da binciken na majalisar wakilain da ya gudanar da binciken domin samo cikekken hujja da zai baiwa majalisar dama tumbuke shugaban daga kan kijeran shugabancin kasar ta Amurka.

An bukaci gwamnatin tarayya da ta dakatar da aniyarta na baiwa Jami o I cin gashin kansu.

Image
An kirayi gwamnatin tarayya da ta janye aniyarta na baiwa Jami o I cin hashin kansu domin kaucewa yabarbarwar ilimi a fadi kasan nan. Shugaban kungiyar malamain Jami o I a Najeriya ASUU shiyar Jami ar Modibbo Adama dake yola Dr El Maude Jbril ne ya yi wannan kira a zantawarsa da manema labarai a yola. Dr El Maude irin cin gashin da yakamata a baiwa Jami o I shine basu damar daukan ma aikata da suka kware da Kuma tsara yadda zasu gudanar da lamaransu yadda ya kamata. Don haka bai kamata ace gatsau kawai gwamnati tace zata baiwa Jami o I cin gashin kansuba. Kuma kamata yayima ta zauna da Jami o I su tattauna kafin daukan mataki da yakamata. Dr El Maude yace daukan mataki irin wannan zai kawo komabaya matuka dangane da koyarwar Jami o I a fadin Najeriya Dan haka gwamnatin tarayyar ta zauna tayi tunani Mai zurfi dangane da wannan aniyatata. El Maude yace wannan ya nuna cewa Rance da gwamnatin taray

An shiryawa mata yan Jarida horo na kwanaki uku a yola.

Image
Daga Ibrahim Abubakar yola Wata kungiya maizaman kanta mai gudanar da aiyukan cigaba OISD ta kaddamar da fara horas da mata yan jaridu a wani mataki na inganta aiyukan mata a kafafen yada labarai. An dai kadamar da horon ne a Jami ar Amurka dake Najeriya dake nan yola wato AUN mai taken zata iya. Mata yan jarida wadanda aka zakulosu daga ahiyar arewa masaugabas domin ganin an samu daidaito da kuma inganta aiyukan aikin jarida ga mata. A jawabinsa Babban darekta kungiyar Mr Jamilu Yusuf ya baiyana cewa ana gudanar da wannan horanne tare da hadin gwiwar sashin harkokin yada labarain ofishin jakadançi Amurka dake Abuja. Jamilu Yusuf yace sun dauki matakin hakane domin karawa matan kwarin gwiwa cigaba da aiyukansu na jarida yadda yakamata. Shima a naahi bangaren shugaban sashin harkokin yada labarai na ofiahin jakadancin Amurka dake Abuja Mr Robert Gabor ya baiyana cewa ofishin jakadancin na Amurka a shirye take domi

Shugaban kasar Koriya ta Arewa ya gana da takwaransa na Rasha.

Image
kasar Koriya ta Arewa Kim Jong Un ya gana da sugaban kasar Rasha Vladimir Putin a kasar Rasha biyo bayan Ziyaran da ya Kai a Moscow. Shuwagabanin kasashen biyu dai sun tattauna batutuwa da dama ciki harda batun makaimai.a yayinda Rashan ke cigaba da yaki da kasar Ukraine. Sai dai shuwagabanin sun misanta ikirarin da Amurka tayi na cewa kasashen na tattauna batun cinikayyar makamaine a tsakanin su. Dangane yakin da Rashan keyi da Ukraine.

An bukaci masu anfani da kwale kwale da su kasance suna maida hankali wajen anfani da kwale kwale.

Image
An shawarci masu amfani da kwale kwale da sukasance masu yin daka tsantsan a duk lokacinda suke gudanar da aiyukansu domin kaucewa aukuwar hatsari akan koguna. Sarkin ruwan Gerio Alhaji AbdulRazak Abubakar ne ya bada wannan shawara alokacin da yake tsokaci dangane da hatsarin kwale kwale da aka samu a wasu kananan hukumomi dake jahar Adamawa Alhaji AbdulRazak Abubakar yace ya kamata matuka kwale kwale su san yawan mutane da zasu rinka deba a cikin kwale kwale da Kuma yawan kaya da zasu rinka lodawa. Alhaji AbdulRazak yace kowane kwale kwale akwai daidain kayan da yakamata a sanya masa dama yawan mtane da yakamata a diba, don haka masu amfani da kwale kwalen su maida hakali sosai wajen aiki da kwale kwalen a Koda yaushe. Ya Kuma kirayi gwamnatin jahar da sukasance masu Sa ido akan harkokin yadda ake gudanar da aiyukan kwale kwalen a fadin jahar baki Daya. Domin ganin an samu cigaba yadda yakamata. In za a iya tunawa

An kirayi kamfanoni masu zaman kansu da su maida hankali wajen daukan matasa aiki.

Image
A wani mataki na rage aikinyi a tsakanin matasa a Najeriya an kirayi kamfanoni masu zaman kansu da su maida hankali wajen deban matasan aiki domin Samar da zaman lafiya dama cigaba mai daurewa a tsakanin Al umma baki Daya. Alhaji Auwal Usman Kuma shugaban kamfanin Auwalus Business Concept kana shugaban kungiyar masu sanar P O S a jahar Adamawa ne yayi wannan kira a lokacin da yake jawabi a wurin tantancewar da zasuyiwa matasa domin samar musu da aikinyi. Alhaji Auwal Usman ya baiyana cewa samarwa matasan aikinyi Wanda acewarsa hakan zai taimakawa matasan rage radadin rashin aiki da suke fama da shi, don haka akwai bukatar a maida hankali wajen samarwa matasan sana o I da zasu dogara da kansu. Da yake jawabi dangane da dalilimsu na daukan matakin diban matasan Alhaji Auwal yace sun dauki matakin hakane duba da irin yanayi da ake ciki na matsalar rayuwa da Kuma

Alhaji Usman Abubakar ya jajantawa iyalen wadanda suka gamu da ajalinsu sakamokon kifewar da kwale kwale yayi a kan kogin Rugange.

Image
Alhaji Usman Abubakar Wanda akafi sani da Manu Ngurore ya jajantawa iyalen wadanda suka rasa Yan uwansu sakamokon kefewar kwale kwale a ruwan Njuwa dake rugange a karamar hukumar yola ta kudu a jahar Adamawa. Alhaji Manu Ngurore ya baiyana lamarin a matsayin Babban rashine ga Al ummar jahar Adamawa ba ga rugange Ka waiba. Ya Kuma yiwa adu ar Allah madaukakin sarki ya jikan wadanda suka rasu ya gafarta musu. Wadanda suka jikkata Kuma Allah ya basu sauki. Ya Kuma Kara da cewa Allah ya baiwa Yan uwan wadanda suka mutu jimre hakurin rashin da sukayi Harwa yau Allah Manu Ngurore ya jajantawa iyalen Bello Liman Wanda Shima ya rasu jiya biyo bayan gajeruwan jinya da yayi yayi Adu ar Allah ya jikanshi da rahama. Ya Kuma jajantawa gidan rediyo Nass bisa rashin ma aikacinsu da sukayi wato Bello Liman. Bello Liman kafin rasuwarsa dai ma aikacin gidan rediyo Nass ne.

Àn bukaci masu rike da masarautun gargajiyà da su bada tasu gudumawa wajen wanzar da zaman lafiya dama hadinkan Al umma.

Image
An kirayi masu rike da masarautun gargajiyà da sukasance masu gudanar da yin dukkanin abunda zaikawa hadin Kai dama zaman lafiya a tsakanin Al umma bak Daya. Hakimin Girei Kuma Uban Doman Girei Dr Ahmed Mustafa ne yayi wannan kira a lokacinda ya marabci tawagan ziyaran godiya da aka Kai masa a fadarsa dake karamar hukumar ta Girei a jahar Adamawa. Babban sakataren Hukumar jindadin Alhazai na jahar Adamawa Mallam Salihu Abubakar nedai ya jagoranci tawagan Kai ziyaran godiyar boyon bayan da ya baiwa Alhaji Adamu Ahmed sarautar wakilin Alhazain karamar hukumar ta Girei. Hakimin yace masu rke Sa masarautun gargajiyà suna da muhimmiyar rawa da zasu iya takawa wajen Samar da zaman lafiya da Kuma cigaban kasa. Don haka akwai bukatar Suma su bada tasu gudumawa wajen gina kasa. Ya Kuma baiyana cewa bisa cancantarsa da Kuma irin gudumawar da ya ba