Posts

Showing posts from October, 2023

Hukumar yan sanda na rike da wani maishekaru 75 da kokarin yiwa yar shekaru 25 fyade a jahar Adamawa.

Image
A yunkurinta na dakile aikata matsalar Fyade a fadin jahar Adamawa rundunan yan sandan jahar tana tsare da wani mutum dan shekaru 75 da haifuwa bisa zarginsa da yunkurin yiwa wata yar shekaru 25 fyade a kauyen Mukuvinyi dake cikin karamar hukumar Hong a jahar Adamawa. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Ngurije ne ya baiyana haka a wata sanarwa da yarabawa manema labarai a yola. Wanda ake zargin mai suna Daniel Jaja yayi kokarin aikata fyaden ne biyo bayan gayyata da yayiwa yarinya zuwa gidansa, wanda kuma hakan yasa ya samu damar ganin zai aikata mata fyade, Bincike da aka gudanar ya baiyana cewa bai samu damar aikata fyadenba saboda yarinyar tayi amfani da reza wajen jimasa a gabansa, wanda hakan yasa yarinyar ta barshi da rauni wanda a yanzu hakama yana kauce a asibiti domin jinya. Kwamishinan yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola. yayi A

Hukumar masuyiwa kasa hidima ta NYSC shawarci direbobi dangane da tafiye tafiyen dare.

Image
A kokarinta na magance matsalar tafiyar dare hukumar masuyiwa kasa hidima wata NYSC ta daukin aniyar wayarwa direbobi kai dangane da tafiye tafiyen dare. Ko odinatan hukumar a jahar Taraba Anthony Nzoka ne ya baiyana haka a lokacinda ya jagoranci tawagan masuyiwa kasa hidma zuwa tashan motoci domin wayarwa direbobi kai da su kaucewa tafiya dare. Tawagan sun ziyarci Babbar tashar jaharTaraba domin fadakar da fasinja dama direbobi dangane da matsalar da tafiyar ke tartare da shi. E Tawagan dai sun rarraba Kansu domin ganin sun isar da sakon yadda ya kamata a fadin jahar inda suka bukaci direbobin dama fasinja da sukasance masu kare rayukansu ta kaucewa tafiyar dare inda aka shawarci matafiya da su hakura da zaran Shida na gamma in yayi. Ko odinaton ya kirayi direbobi da su tsaya da zaran suna jin barci musammanma in sukazo wucewa a kusa da ofishin yan sanda, bariki

Kungiyar ma aikatan majalisar dokokin jaha PASAN ta bi sahun uwar kungiyar wajen shiga yajin aiki.

Image
Kungiyar ma aikatan majalisar dokokin jihohi shiyar jahar Adamawa PASAN tabi sahun uwar kungiyar ta kasa wajen shiga yajin aikin Illa masha Allah na kasa baki daya, biyo bayan rashin aiwatar da kidirin dokan cingashinkansu dangane da kudi majalisar dokokin jihohi wanda yake cikin kundin dokan tarayya Najeriya. Shugaban kunguya ta PASAN a jahar Adamawa Idris Sali ne ya baiayana haka a lokcin ya jagiran taron da kungiyar ta gudanar a harabar majalisar dokokin jahar Adamawa, yace rashin aiwatan da dokan da gwamnati tayi wanda hakan yasa suka dauki tsawon lokaci suna dako. Shugaban yace duk dacewa anacigaba da tattaunawa a tsakanin kungiyar da gwamnati a matakim kasa wanda suke sa tsammanin cewa za a samu sakamokon da zata haifar da da mai ido domin kungiyar gwamnoni sun fara duba lamarin. Ya kuma koka da yadda wasu jihohin suna fuskantar irin wadannan kalubale na rashin aiwatar da basu yancin gaahin ka

Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta lashi takwabin dakile aikata ta addanci a fadin jahar ta Adamawa.

Image
A kokarinta na dakile aiyukan ta addanci a fadin jahar Adamawa rundunan yan sandan jahar yanzu haka tana tsare da wata mota mai dauke da rijistan Numba GME 235 AE wanda kuma an gano wasu kayaki guda uku a cikin motar. An samu nasaran kama motan ne a lokacinda Jami an yan sandan ofishin yan sanda dake Yolde Pate ke gudanar da sintiri akan titin da ta hada Yola da Yadim. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da yarabawa manema labarai a Yola, fadar gwamnatin jahar Adamawa. Sanarwan ta baiyana cewa a yayinda direbab motar ya hangi Jami an tsaro sai yayi kokarin kaucewa da ya samu matsin jami an tsaro sai ya tsallaka ya bar motar ya gudu. An gono wasu kayaki a cikin motar da suka hada da tsarka, makulli, wato kwado, da dai sauransu. Wanda kuma ana zargin yana amfani da sune wajen yin garkuwa da mutane.

Kungiyar yan Jarida a Najeriya shiyar jahar Adamawa ta taya Gwamna da mataimakiyatsa murna samun nasara a kotun sauraren koke koken zaben gwamna.

Image
Biyo bayan da kotun sauraren koke koken zaben gwamna Wanda tayi zamanta a yola Kuma ta yanke hukunci baiwa gwamna maici wato Ahmadu Umaru Fintiri nasara. Alkalai uku karkashin jagorancin maishariya Theodora O Uloho inda suka yanke hukunci cewa gwamna Ahmadu Umaru Fintiri ne halacceccen zaben gwamna jahar Adamawa. Hakan yasa kungiyar yan Jarida a Najeriya N U J shiyar jahar Adamawa tana taya Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri murnan nasara da ya samu a kotun sauraren koke koken zaben gwamna wacewar kungiyar dai wannan hukunci nasarace ga Al ummara jahar Adamawa. Nasaran gwamna Fintiri ya nuna cewa sashin shariya na nan daram wajen gudanar da adalci wa Al umma da kuma bin doka da oda a jahar dama kasa baki daya. Kungiyar ta baiyana haka ne a sakonta na taya murna ga gwamna Ahmadu Umaru Fintiri da fitar dauke da sanya hanun sakateren kungiyar ta N U J a jahar Adamawa Fedelis Jockthan. Da wannan ne kungiyar take t

An baiyana cewa nasaran da gwamna Fintiri yayi a kotu nasarace ga Al ummar jahar Adamawa.

Image
Usman Abubakar wanda akafi sani da Manu Ngurore yana Mai taya Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri murna yin nasara a kotu sauraro koke koken zaben gwamna a zamanta na anan Yola. Alhaji Usman Abubakar Wanda shine mataimaki na musamman akan harkokin noma da sana o I na gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jahar Adamawa.. Alhaji Usman yace wannan nasara da gwamna yayi ya nuna cewa Yan jahar Adamawa basuyi zaben tumun dareba domin kuwa an basu abinda suka zaba kasancewa gwamna Yana gudanar da aiyukan cigaban jahar. Alhaji Usman yace ba Wanda ya dace ya Mulki jahar kamar Ahmadu Umaru Fintiri saboda yadda ya gunara da aiyuka daban daban harma da bada Ilimi kyauta wa Al ummar jahar tare da bunkasa bangarori daban daban da suka hada da Noma, kiwon lafiya, koyawa matasa da mata sana o I daban daban domin dogaro da kansu. Ya Kuma kirayi daukacin Al ummar jahar Adamawa da sucigaba da baiwa gwamna Ahmadu Umaru Fintiri hadin Kai d

Rundunan yan sandan a jahar Ogun tana tsare da dalube biyu bisa zarginsi da cinnawa kayakin makarantansu wutan.

Image
Rundunan yan sandan jahar Ogun yanzu haka tana tsare da dalube biyu da ake zargi da cinnawa kayakin makarantarsu wuta, wato makarantar Firamare dake Isheri Olofin a jahar ta Ogun. Daluben da ake zargin sun hada da Wahis Musa dan shekaru 6 da haifuwa da kuma Malik Illiasu shi kuma yana da shekaru 9 da haifuwa dukkaninsu mazauna Isheri Olofin ne. Kakakin rundunan yan sandan na jahar Ogun Omolola Odutola ne ya sanar da haka a wata sanarwa da yarabawa manema labarai a Abeokuta fadar gwamnatin jahar Ogun. Kama daluben ya biyo bayan rahoton da ofishin yan sandan yankin Ojodu- Abiodun ya samu cewa Wahis Musa da Malik Illiasu sun shiga wani aji da ba a kulleba inda suka rinka tattara takardun makarantar a wari guda nan take suka cinnawa takardun wuta. Wanda kuma kawo yanzu ba a kai ga sanin yawan barnan da wutan tayiba. Daga samun rahoton haka Jami an yan sandan yank

Kotun sauraren koke koken zabe ta yi watsi da karanda sanata Aishatu Binani ta shigar.

Image
Kotun sauraron koke koken zaben gwamna a jahar Adamawa a zamanta a yola fadar hwamnatin jahar Adamawa a asabardin nan tayi watsi koke koken da sanata Aishatu Binani ta shigar mata na kalubalantar gwamna Ahmadu Fintiri. Yar takaran gwamna na jam iyar APC sanata Aishatu Dahiru Binani ta shigar da kara inda take kalubalantar zaben gwamna wanda hukumar zabe ta gudanar a ranan 18-3-2023 Sanata Aishatu Binani dai tana kalubalantar nasaran da hukumar zabe ta aiyana gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jam iyar PDP ne ya lashe zaben gwamna da aka gudanar gudanar. Da take yanke hukunci shugabar Kotun sauraren koke koken maishariya Theodora Obi Uloho tayi watsi ta karan da sanata Aisha Binani ta shigar mata tare da tabbatar da gwamna Ahmadu Umaru Fintiri a matsayin wanda yayi nasaran lashe zaben. A ranan 18-3-2023 hukumar zabe mai zam

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri ya yaba da hukuncin da kotun sauraren koke koken zabe ta yanke.

Image
Gwamnan jahar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri ya bada yakinin cewa sashin shariya a Najeriya itace dama da kaahe ga jama a. Gwamna Ahmadu Fintiri ya baiyana hakane a lokacinda yake mayar da martani dangane da hukuncin da kotun sauraren koke koken zabe ta yanke wanda ta baiwa gwamna Fintiri da cewa shine yayi nasara a zaben gwamna da aka gudanar . Acewar gwamna Fintiri yace abinda da ya shaida a yau shine gaskiya tayi halinta kuma ya nuna cewa sashin shariya na gudanar da aiyukanta yadda ya kamata domin cigaban kasa dama al umman Najeriya. Gwamna Fintiri yace wannan shariya ya kawo karshen duk wasu shakku dangane da zaben gwamna da aka gudanar saboda haka za a cigaba da gudanar da aiyukan cigaban al ummar jahar ta Adamawa baki daya. Gwamnan ya kuma godewa Alkalain da suka jagoranci zaman kotun sauraren koke koken zaben k

Rundunan yan sandan jahar Gombe tayi nasaran kama wadanda ake zargi da aikata laifuka daban daban a fadin jahar.

Image
Rundunan yan sandan jahar Gombe ta laahi takwabin inganta tsaro domin kare rayuka da kuma dukiyoyin Al umma a fadin jahar Gombe, acewar rundunan dai zatayi aiki kafada da kafada da shuwagabanin al umma dama masu ruwa da tsaki domin ganin anbi doka da oda a fadin jahar baki daya. A yanzu haka ma rundunan tana tsare da wani matashi da ake zargi da kaahe wata mai suna Hajiya Aisha Abdullahi Aka Damori, da wasu mutane biyu da ake zargi da yin garkuwa da mutane da kuma kisan kai, sai kuma mutane uku da ake zargi da dayin fashi da makami a yayinda biyu kuma ake zarginsu da aikata fyade. Kakakin rundunan yan sandan jahar Gombe Mahid Mu azu Abubakar ne ya baiyana haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a jahar Gombe. Sanarwan ta baiyana cewa rundunan tana tsare da mataahin mai suna Mustafa Adamu Isa wanda akafi sani da (Abbati). Dan shekara 18 da haifuwa wanda ke zaune a anguwar jeka da fari a

Gwamnatin jahar Adamawa ta bukaci da al ummar jahar su maida hankalin wajen yiwa jaha dama kasa adu o i.

Image
Gwamnan jahar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri ya kirayi daukacin al ummar jahar Adamawa, tare da yan uwa da abokan arziki da su kaucewa taruwa da niyar yin bikin ranan haifuwarsa a ranan Jumma a 27-10-2023. Gwamnan Ahmadu Fintiri yace mai makon haka ya kamata ayiwa jahar Adamawa da kasa baki daya adu o I, ya kara da cewa Al umma suna bukatan tainakon gaggawa biyo bayan matsalar tattalin arziki da ake fama da shi sakamokon cire tallafin mai fetur da akayi. Babban sakataren watsa labarai gwamnan Humwashi Wonosiko ne ya baiyana haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a yola. Sanarwa tace mai girma gwamnan yace wannan yanayi da ake ciki na tsadar rayuwa wanda jama a ke fuskata wanda kuma hakan ya shafi tattalin arziki dama tsare tsaren gwamnatin tarayya. Domin magance matsalar a kwai bukatan a hada kai da kuma yin aiki tare d

An kaddamar da fara aluran riga kafain kansar mahaifa wanda za ayiwa yaran mata da shekarunsu ya kama daga 9-14 a fadin jahar Adamawa.

Image
A daidai lokacin da Najeriya ta fara gudanar da gagarumin aikin allurar riga-kafin cutar kansa mahaifa wato Human papillomavirus, HPV, a wani yunkuri na rage radadin cutar sankarar mahaifa, Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jihar Adamawa ya bukaci iyaye da masu kula da su da su baiwa ‘ya’yansu da suka cancanta domin tabbatar da cewa sun samu alurar riga kafi. Gwamna fintiri ya bukaci hakane a lokacin da yake jawabi a bikin kaddamar da aluran rigakafin cutar ta HPV ga duk mata masu shekaru tara zuwa sha hudu a Yola jihar Adamawa. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri wanda mataimakiyar gwamnan jihar Adamawa, Farfesa Kaletapwa George Farauta ta wakilta ta yabawa kokarin hukumar kula da lafiya matakin farko na jihar Adamawa da ma’aikatar lafiya ta jihar bisa rawar da suke takawa wajen gudanar da ayyukan tun kafin a fara aiwatar da ayyukan riga kafin, sannan ya bukaci iyaye da masu kula

Kungiyar yan kasuwan Yankin Arewacin Najeriya tace itakam ba wani rikicin shugabancin a cikin kungiyar.

Image
An bukaci ya yan kungiyar yan kasuwar arewacin Najeriya wato Arewa Traders Association of Nigeria ATAN da su kasance masu hada kansu a koda yaushe domin samun cigaban kunguyar a Najeriya baki daya. Shugaban kungiyar a shiyar jahar Bauchi kuma sakataren tsare tsaren kunguyar na yankin arewa masau gabashin Najeriya Alhaji Abdullahi Y Muhammad wanda akafi sani da (Abdallah Caps). ne ya baiyana haka a lokacinda yake jawabi dangane da kutsen shugabanci da wasu keyiwa kungiyar a matakin kasa. Alhaji Abdullahi Y Muhammad yace ba dai dai bane ace ana samu rashin dai dai to a tsakanin shuwagabani kungiyar wanda hakan zaikawo koma bayan aiyiukan kungiyar.don haka ya kamata shuwagabanin kungiyar sukasance tsintsiya madaurinki daya domin kai kungiyar tudun na tsira. Alhaji Abdullahi kira yayiwa shuwagabanin da sukasance masu hada kasu da kuma yin dukkanin abinda suka dace domin kawowa yan kasuwa cigaba domin bunkasa ha

Rundunan yan sandan jahar Adamawa tasha alwashin inganta tsaro a fadin jahar Adamawa.

Image
A wani mataki na samar da dabaru dama inganta tsaro rundunan yan sandan jahar Adamawa ta bauyana aniyarta na hada kai da masarautun gargajiya, yan banga mafarauta da dai sauranasu domin dakile aiyuka ta addanci a tsakanin Al umma. Kwamishinan yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola ya tabbatar da cewa rundunan a shirye take ta takawa dukkanin aiyukan ta addanci birki dama sauran kalubalen tsaro a fadin jahar ta Adamawa baki daya. Kwamishinan ya baiyana hakane a ranan talata 24-10-2023 a lokacinda yake jawabi a ofishin rundunan dake Karewa a cikin karamar hukumar yola ta arewa a ganawa da yayi da masu ruwa da tsaki da manyan Jami an yan sandan harma da yan banga domin yaki da masu aikata laifuka a fadin jahar. Kakakin rundunan

An yabawa Hajiya Aishatu Binani

Image
An yabawa sanata Aishatu Dahiru Binani bisa taimakawa da kuma kyaututtuka da takeyiwa al umma a bamgarori daban daban. Alhaji Adamu Dan Wanzam uban kungiyar yan gwari a jahar Adamawa ne yayi wannan yabo a ganawarsa da manema labarai a yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Alhaji Adami yace ba abinda zaice sai dai godiya ga Allah madaukakin sarki tare da godewa sanata Aisha Binani bisa kyautar mota da ya samun. Ya kuma yimata adu ar Allah madaukakin sarki ya biya mata dukkanin bukataunta na Alhari ya kuma rabata da dukkanin shari, Allah ya kuma bata nasaran rayuwa mai Albarka. Adamu ya kuma goewa manyan Jami an ta irinsu Alhaji Salihu Baba Ahmed, Alhaji Isa Bakalci, Manchi, Maulud, da dai sauransu wanda acwarsa mutane ne da suke da manufa mai kyau saboda yana mika godiyarsa ga jinjina a garesu baki daya.

An bukaci membobin kungiyar Yan kasuwar Arewacin Najeriya da sukasance masu hada kansu.

Image
Biyo bayan ta kaddaman shugabanci da ya kunno kai a cikin shugabanci kungiyar yan kaauwar arewacin Najeriya wato Arewa Traders Association a Nigeria, ATAN a matakin kasa hakan yasa shuwagabanin kungiyar a matakin jihohi ke nuna goyon bayansu ga shugaban kungiyar na kasa Alhaji Muhammed Ibrahim 86 wanda a cewarsu su suka sani a matsayin zababben shugaban kungiyar ta kasa kamar yadda dokan kungiyar ya tanada. Shugaban kungiyar yan kasuwa a arewacin Najeriya shiyar jahar Kogi Dr Umar Muhammed ne ya baiyana haka a zantawarsa da manema labarai dangane da matsalolin rarrabuwar kai da ake samu a kungiyar. Dr Umar Muhammed yace suma suna zaune ne kwatsam sai sukaji wai ga wasu da aka baiyanasu a matsayin shuwagabanin kungiyar Arewa Traders Association of Nigeria wanda kuma basu San da suba domin kuwa ba abi dokan kungiyarba asalima wannan shine ake kira sojan gona, ko kuma shigan biltu. kuma abin manakinma shine wanda yake ikitari

Wadanda ake zargi masu garkuwa da mutane ne sun shiga hanun runduna yan sandan jahar Adamawa.

Image
N Rundunan yan sanda a jahar Adamawa tayi nasaran cafke mutane shida da ake zargi da yin garkuwa da wani yaro dan shekara tara harma sun nemai kudin fansa na nera milyon biyar a cikin karamar hukumar Mubi ta kudu dake jahar Adamawa. Wadanda ake zargindai dukkaninsu mazauna garin Mubi ne a anguwar Kaba dake kan titin zuwa karamar hukumar Maiha daga Karamar hukumar Mubi ta kudu. Wadanada ake zargi da yin garkuwa da yaron mai suna Mustafa Ibrahim a ranan 18-10-2023. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Ngurojene ya sanar da haka a wata sanarwa da rabawa manema labarai a yola. Sanarwan tace an samu nasaran cika hanu da wadanda ake zarginne biyo bayan koke da suka samu daga mahaifin yaron a ranan 19-10-2023 cewa wasu da ba asan ko siwayeba sun kutsa gidansa da aniyar sayan Zobo Juice inda sukayi awungaba da dansa mai shekaru sha tara. Kawo yanzu dai kwamishinan yan sandan jahar Adamawa Afolabi

Rundunan yan sandan Najeriya zata gudanar da taro domin inganta tsaro a fadin Najeriya.

Image
A kokarinsa na tabbatar da inganta tsaro a fadin Najeriya, Babban sifeton yan sandan Najeriya Kayode Adeolu Egbetokun ya gudiri aniyar ganin an samar da wadaceccen tsaro domin aiwatar da tsarin gwamnatin tarayya na samar da tsaro da dai sauransu. Hakan yasa Babban sifeton ya shirya taro na musamnan da za a yi da manyan Jami an yasandan dake fadin Najeriya wanda ana saran za a fara taro daga ran 30-10-2023 zuwa ran 1-11-2023 a Owerri dake jahar Imo. Kakakin rundunan yan sandan ta kasa ACP Olumuyiwa Adejobi ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar wanda aka rabawa manema labarai a Abuja. Taron wanda zai hada kan manyan Jami an yan sandan da suka hada da mataimakan Babban sifeton yan sandan Najeriya, kwamishinonin yan sandan,dama sauran wasu hukumomin tsaro da suma ake saran zau halarci taron. Wanda kuma haka zai bada dama ga rundunan yan sandan

Wani yaro ya rataye kansa a jahar Adamawa.

Image
Rundunan yan sanda a jahar Adamawa tace ta samu rahoton cewa wani yaro ya rataye kansa a anguwar Runde Baru dake cikin karamar hukumar yola ta arewa a jahar Adamawa. Kakakin rundunan yan sandan a jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar a yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Sanarwan tace a yanzu haka rundunan tana aiki kafada da kafada da Jami an kiwon lafiya domin bankado musabbabin da yasa yaron ya rataye kansa. Kwamishinan yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola ya kirayi daukacin Al ummar jahar ta Adamawa da sukasance masu taimakawa rundunan da wasu bayanain sirri domi bata damar gudanar da aiyukanta yadda ya dace.

Babu matsalar shugabanci a cikin kungiyar yan kasuwan yankin arewacin Najeriya .....Gambo Uban Nura.

Image
An baiyana cewa kungiyar yan kasuwar arewacin Najeriya na nan daram kanta a hade yake ba wani matsalar tattare da kungiyar. Shugaban kungiyar na shiyar jahar Adamawa Alhaji Gambo Uban Nura ne ya baiyana haka a lokacinda yake magana dangane da kutse da wasu keson yiwa kungiyar a matakin kasa, wadanda kuma bazasu samu nasaraba da yardan Allah. Alhaji Gambo Uban Nura yace wasu ne kurum ke kokari kawo rudani a shugabancin kungiyar. Saboda haka ba abinda ya samu kungiyar komai yana tafiya dai dai karkashin jagorancin Alhaji Muhammed Ibrahim 86 kuma ba abinda zai taba shugabancinsa har sai ya kammala wa adinsa na shekaru hudu akan shugabancin kungiyar a matakin kasa. Gambo Uban Nura yace duk da cewa ba a rasa wasu matsaloli a kungiyar to Amman sukam Alhaji Muhammed Ibrahim 86 suka sani a matsayin shugaban kungiyar yan kasuwa na arewacin Najeriya saboda su suka zabe

Gwamnatin jahar Kano ya kudiri aniyar tura dalube Sama da dubu Daya kasashen waje domin karo karatu.

Image
jahar Kano Abba Kabir Yusuf yace gwamnatinsa zata dauki nauyin karatun dalube akalla 1,001wadanda zasuyi karantun digiri na biyu a Jami o I daban daban dake fadin duniya. Gwamnan ya baiyana hakane a lokacin kaddamar da shirin Kai dalube karatu kasashen waje karatu Wanda ya gudanar a gidan gwamnati dake Kano. Gwamnan yace tawo da Shirin Samar da gurbin karo karatu a kasashen waje yana daga cikin cika alkawarin da yayi a lokacinda yake Neman zabe.wanda Kuma yace lamarine da ya rataya akan gwamnati. Ya Kuma baiyana cewa wadanda suke dauke da digiri na farkone zasu ci gajiyar Shirin da zasuyi karatu a kasashen Indiya, da dai sauransu. Wadanda suka anfana da Shirin sun nuna godiyarsu da Jin dadinsa dangane da damar da aka basu domin samun gurbin karo karatu a kasashen waje.

Kasar Israila ta kai hari akan mujami a a Gaza.

Image
Mutane da yawa ne dai suka samu mafaka a harabar wata muja mi a a yankin zirin Gaza biyo bayan da jirgin yakai kasar Isla ila ya kai hari akan mujami at, harin da yayi sanadiyar mutuwar mutane da dama. Kamar yadda ministan harkokin cikin gidan Gaza ya baiyana. Kawo yanzu dai mutane akalla 1150 ke amfani da mujami ar dake da tsawon tarihi a garin na Gaza. Mabiya addinin kirista da mabiya adinin musulunci da dama ne ke samu mafaka a wuraren ibadu a yankin na Gaza. Rundunan sojin kasar ta Israila dai tace jirgin yaki ya yi kokarin kai hari a cibiyoyi dake kai hare hare da makamai masu lizami inda roka ya fadi aka mujami ar. A cikin kwanaki sha uku da suka gabatane dai musulmai da mabiya addinin Krista suka fice daga Gaza domin tsira da rayuwarsu biyo bayan hare haren da aka kira na ramukon gayya da Israila ke kaiwa a garin na Gaza.

Gidauniyar Attarahum ta yabawa sanata Aisha Dahiru Binani.

Image
Kungiayr Attarahum Foundation na mika godiyarta ga sanata Aishatu Dahiru Binani bisa kyautar mota kiran foma da ta baiwa kungiyar. Kungiyar ta Attarahum Foundation tayi yabon ne a wata sanarwa da ta fitar dauke da sanya hanun shugaban kunguyar a jahar Adamawa Malam Mukhtar Dayyib a. yola, fadar gwamnatin jajar Adamawa. Kungiyar a madadin shuwagabanin kungiyar dama membobin kungiyar na mika dinbin godiyarsu da farin cikinsu dangane da wannan taimako da sanata Aisha Binani tayi musu. Sanarwa tace gidauniyar ta nuna goyon bayan ta tare da jinjinawa sanata Aisha Binani bisa na mijin kokari da takeyi na taimakwa kungiyoyi dama dai dai kun al umma baki daya. Kunguyar ta kuma gudanar da adu o i na musamman domin nemana taimakon Allah da ya bada nasara a dukkanin abinda tasa agaba.

Kungiyoyi masu zaman kansu sun nemi da a bunkasa harkokin noma .

Image
Wasu kungiyoyi masu zaman kansu sun nemi da gwamnatin jahar Adamawa da ta kasance tana sanya ido kan aiyukan harkokin noma dama gudanar da shirye ahiryen abinda ya shafi harkokin noma domin inganta harkar noma a fadin jahar. Shirin wanda zai gudana kakashin hukumar inganta harkokin noma a Najeriya, IAA a cikin shekaru biyar da rabi wanda zai lashe dalan Amirka milyon 15.8 tare da hadin gwiwar cibiyar bunkasa harkan noma ta kasa da kasa IITA tare da cibiyar binciken dangane harkokin tsiro na kasa da kasa ICRISAT. Shirin zai taimakawa marassa galihu musammanma wadanda rikicin boko haram ya shafa saboda haka akwai bukatar a kara musu kwarin gwiwa cigaba da bunkasa harkokin noma yana daga cikin aniyar hukumar USAID domin ganin an farfado da tattalin arzikin arewa masau gabashin Najeriya biyo bayan tasku da ya shiga sakamokon hare haren masu tada kayan baya. Mataimakin shugaban kungiyar ta IAA Mr Olukayode Fa

An ja hankalin kwamishinoni wajen gudanar da aiyukan cigaban jahar Adamawa.

Image
Mataimakiyar Gwamnan jahar Adamawa, Farfesa Kaletapwa Farauta ta karanto sabbin komishinoni da aka nada dokar hana tarzoma. Hakan na kunshene a a cikin wata sanarwa wanda sakataren watsa labarai mataimakiyar gwamna Hussaini Hammangabdo ya fitar a yola. Farfesa ta shaidawa kwamishinonin cewa da suyi amfani da mukaminsu wajen cigaban jahar baki daya. Da take jawabi a wurin wani taron da kayi da kwamishinonin a yola Farfesa Farauta tace gwamnati tana iya kokarinta domin gudanar da aiyukan cigaban jahar. Tare da kiransu da su gudanar da aiyukan su yadda ya kamata a wani mataki na cigaban jahar. Ta kuma baiyana cewa kyakkawar gwamnati da aka zaba tana yin duk abinda zai kawo cigaba dama zaman lafiya. Tace su sani gwamnati tana da manufofin da takeso ta cimma wadanda suka hada da inganta tsaro, bada ilimi kyauta, samarwa matasa aikinyi, saboda akwai bukatar baiwa gwamnati hadin kai da goyon baya domin ganin ta samu nasaran

Takaitattun labarain duniya daga shafin Al Nur hausa.

Image
Takai tattun labarain duniya. Daga shafin Al Nur. Bari mufara daga yanakin zirin Gaza yankin da kasar Israila ke baiwa hamata iska da falasdinawa. Ibrahim Alagha da shi da uwar gidansa sunkasance a Garin na Gaza ne domin su gudanar da hutunsu Amman sai akayi rashin sa a biyo bayan hare hare da jiragen yakin Israila ke kaiwa a yankin na zirin Gaza lamarin da ya sasu neman mafaka. Ma auratan biyu dai sun fitone daga wani gari da ake kira Irish tare da yaransu guda uku wanda kuma sunzo da sune domin su nuna musu garin su na asali kuma suga yan uwansu falasdinawa. Yana yin yaki da ake ciki yasa basu sadu da yan uwan nasuba sakamokon kai hare hare da kuma fashewar bamabumai a yankin na zirin Gaza. A kasa Ghana kuwa wata matace mai suna Awusifa Kagbitor ta baiyana yadda ambaliyar ruwa yayi mata sanadiyar asaran kayakinta masu yawa. Tace tana zaune kwatsam sai taga ruwa yana mala

Gwamnatin jahar Gombe ta taya Alhaji Jalal Arabi murnan samun mukamin shugaban hukumar aikin Hajji ta kasa wato NAHCON.

Image
Gwamnan Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya yaba da yadda aka nada dan jahar ta Gombe Alhaji Jalal Arabi wanda shugaban kasa ya Bola Tinubu ya nada a matsayin shugaban hukumar aikin Hajji ta kass wato NAHCON. Gwamana Muhammadu Yahaya ya yaba tare da godewa shugaban kasa Bola Tinubu bisa nada dan Asalin jahar Gombe Alhaji Jalal Arabi inda ya baiyana nashi a matsayin wanda ya cancanta kuma mutunne wanda yasan makaman aiki. Gwamnan ya baiyana hakane a wata sanarwa wanda darectan watsa labarain gwamnan Ismaila Uba ya fitar a jahar Gombe. Sanarwa tace Alhaji Jalal yana da kyakkyawa tarihi wanda yayi ritaya a matsayin babban sakatare tararayya. Gwamnan ya shawarceshi da ya gudanar da aiyukansa bil hakki da gaskiya domin samun cigaban hukumar yadda ya kamata. Sanarwan ta kara da cewa nada Alhaji Jalal Arabi abun alfahari ne ga jahar Gombe kuma jahar zataji kunyaba dom

Rundunan yan sanda a jahar Adamawa tasha alwashin zakula masu aikata laifuka daga maboyarsu dake fadin jahar.

Image
A kokarinta na dakile aiyukan ta addanci a fadin jahar Adamawa rundunan yan sandan jahar tayi nasaran kama wani mutum mai shekaru talatin da haifuwa mai suna Shuaibu Abubakar kuma an samu nasaran cafkeshi a wani samamen hadin gwiwar yan sandan da mafarauta suka kai a mabuyar yan ta addan. Maihulda da jama a na rundunan yan sandan a jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a yola. Sanarwa tace akwai wani da ake zargi dake Tambo wanda kuma yana cikin jerin sunaye wadanda ake neman ruwa a jallo. Rundunan ta kuma gano bindiga kiran Ak 47 da kuma arbarushe 16 a wurin wadanda ake zargi. Kawo yanzu kwamishinan yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola ya baiyana farin cikinsa dangane da nasaran da rundunan tayi. Ya kara da cewa babu maboyar masu data kayan baya a jahar Adamawa domin kuwa rundunan ta dauki dukkanin abinda

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jahar Adamawa ya kirayi kwamishinoni da manyan sakatarori da su bada tasu gudumawa domin cigaban jahar ta Adamawa

Image
Gwamnan jahar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri ya ja hankalin komishinoni da sakatarorin dindindin na jahar da su sa kula kan kudade da suke kashewa a ofisoshin su da ma rawa da suke takawa a matsayin su na manyan jami’an gwamnatin shi. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri yayi wannan kira ne yayin da yake jawabin bude taron karawa juna sani na komishinoni da sakatarorin din din din na jahar mai taken: DAURAWA KAN SHUGABANCI MAI KYAU: MATSALOLI DA KUMA HANGEN GABA WA JAHAR ADAMAWA wanda ya wakana a birnin yola fadar jahar Adamawa. Gwamnan Ahmadu Umaru Fintiri yace ba zai yi haba haba ba gurin kin amincewa da bukatun kudade da za su jefa jahar cikin bashi , tare da jaddada cewa a kokarin gwamnatin shi na kawar da duk wani tarko da zai abka su cikin rashawa, da kuma bullo da wani tsari na fahimtar matakan da zaiiya domin cigaban.jahar Adamawa. Gwamna Fintiri yace a duk lokacin da ya Samu daman gana

Gwamnatin jahar Adamawa ta shawarci hukumomin tsaro da sukasance masu aiki kafada da kafada domin dakile matsalar tsaro a fadin Najeriya.

Image
Gwamnan jahar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri ya bada shawarar yawanta zama tsakanin cibiyoyin tsaro a matsayin daya daga cikin matakan dakile matsalolin tsaro dake addabar kasar nan. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri ya bada wannan shawara ne yayin da yake bude taron daraktocin cibiyar tsaro na farin kaya, DSS karo na goma sha uku da ya wakana a shalkwatar cibiyar tsaron na jahar Adamawa dake yola, fadar jahar. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri ya bada shawarin cewa kamata yayi cibiyoyin tsaro sun rika yawaita zama domin musanyar bayanai, tsara yadda za suyi aiki da ma shawo kan kalubale ko gibi da ake da su domin samar da zaman lafiya da tsaro. Gwamnan yace musanyan bayanai, atisayin hadaka da karawa juna sani tsakanin cibiyar tsaron farar kayan da takwarorin ta zai taimaka matuka gurin samar da cikakken bayanen yanayin tsaro da ake fama da shi a rewa maso gabas, kana atisayin zai karfafa kuzarin yadda za a rika

An bukaci masu rike da mukamai masu bada sharawa gwamna da su riki mukamin da daraja.

Image
Gwamnan jahar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri ya ja hankalin masu mukamin masu bada shawara na musamman da su dauki nadin nasu da muhimmanci domin ci gaban jahar. Gwamnan Ahmadu umaru Fintiri ya baiyana haka ne yayin rantsar da Salisu Zumo a matsayin mai bashi shawara na musamman, a wata biki da ta wakana a ofishin gwamnan dake gidan gwamnati dake yola fadar gwamnati jahar. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri yace gwamnatin shi ta mayar da hankali ne gurin ci gaban yan jahar adamawa ganin a halin yanzu sun fi bukatar haka a kan komai. Gwamnan yace ci gaban al’umma na kan gaba a gwamnatin shi, hakan ya sa ake bukatar masu basira irin su Salihu Zumo su shigo domin taimaka wa gwamnati domin tayi nasara. Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri yace gwamnatin shi ta kudiri anniyar ganin ta daukaka al’ummar jaha zuwa mataki na gaba, tare da Karin cewa gwamnatin tayi nasarori da dama tun daga shigowar t

Sakataren harkokin wajen Amurka ya gana da firaministan kasar Isra ila.

Image
Karo na biyu a litinin din nan ne sakataren harkokik wajen Amurka Antony Blinken ya gana da firaministan kasar Isra ila a garin Tel Aviv. Tun a makon da ta gabatane dai sakateren harkokin kasar wajen Amurka ya gana da firaministan kasar ta Isra ila Benjamin Netanyahu bayan da Hamas ta kaddamar da hare hare masu karfi akan kasar ta Isra ila. Antony Blinnken ya tabbatar da cewa kasar Amurka zata baiwa kasar ta Isra ila goyon baya domin kasar ta kare kanta daga duk wani hari da za a iya kawo mata. Sama da Isra ilawa 1,400 ne dai suka hallaka a kwanaki tara da suka gabata biyo bayan da kungiyar Hamas ta kutsa cikin kasar ta Isra ila ta Gaza tare da kai hare hare lamarin da yayi sanadiyar mutuwar sojoji da fararen hula.

Shelkwatan rundunan yan sandan jahar Adamawa tana tsare da wani da ake zargi da garkuwa da mutane.

Image
Rundunan yan sandan jahar Adamawa a yanzu haka tana tsare da wani matashi dan shekaru 25 da haifuwa mai suna Gaiya Mallam Usman bisa zarginsa da aikata yin garkuwa da mutane. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Ngyroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar a yola fadar gwamnatin jahar. Wanda ake zargin wanda ya fito daga Tambo a cikin karamar hukumar Girei a jahar Adamawa wanda ake zarginsa da wasu mutane hudu da yin garkuwa da mutane uku harma sun karbi kudin fansa nera milyon 8. Sai dai wanda ake zargin ya baiyana cewa shikam dubu 470.000 kawai ya karba cikin milyon 8 daga iyalen wadanda aka yi garkuwa da su kuma ya baiyana cewa yayi amfani da kudaden ne wajen sayan kayakin sawa. Kawo yanzu dai kwamishinan yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola y

Akalla yaran mata dari ne dai suka samu horo kan sana o i dogaro da kai a sansanin yan gudun hijira a jahar Adamawa.

Image
A yayinda ake gudanar da bikin ranan yaran mata ta duniyar a wannan shekara ta dubu biyu da ashirin da uku. Hakan yasa kungiyar Action Health tare da hadin gwaiwar kungiyar raya kasa ta Amurka USAID da kuma Asusun Al umma na majalisar dinkin duniya UNFPA sun horar da yaran mata sana o i daban daban a sansanin yan gudun hijira dake Daware a cikin karamar hukumar Fufore a jahar Adamawa. Bikin na bana mai taken inganta rayuwar yaran mata domin samar da shugabanci da ya dace. Da kuma samarwa yaran mata yancinsu yadda ya kamata. Da yake jawabi dangane da ranan yaran matan ta duniya shugaban sansanin yan gudun hijiran Umar Bappa ya yabawa kungiyoyin bisa wannan taimako da sukayi musu inda yace al ummarsu zasu samu cigaba harma da inganta rayuwarsu. Ardon Daware Umaru Bobbo wanda Ezra Christopher ya wakilta shima yabawa yayiwa

Kamfanin Auwalus Business Concept ya kaddamar da fara Bude asusun ajiya na banking moniepoint

Image
Kamfanin Auwalus Business Concept ya kaddamar da tsarinsa na bude asusun ajiya a Bankin nan na moniepoint wanda hakan yasa jami an kamfanin suna zagayawa ga duk mai saon bude asusun ajiya zai da Jami an da riga dake dauke da alamar sunan kamafin sai ya tuntubesu domin karin bayani ko kuma ya ziyarci kamfanin dake palace dora da ofishin NEPA.

Babban sifeton yan sandan Najeriya zai jagoranci tawagan yan sanda domin halartan babban taron kan tsaro a kasar Amurka.

Image
Babban sifeton yan sandan Najeriya na riko Kayode Adeolu Egbetokun ya jagoranci manyan Jami an rundunan yan sandan domin halartan babban taro da akeyi a hihohin San Diego, da California na kasar Amurka. Wanda za a tattauna batutuwa da dama domin zakulo hanyoyin inganta tsaro a fadin duniya. Kakakin rundunan yan sandan na kasa ACP Olumuyiwa Adejobi ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar a Abuja. Taron wanda tunin aka fara daga ranan 14 zuwa 17 ga watan oktoban nan da muke ciki, wanda kuma za a samu halartan manyan Jami an yan sanda daga sassa daban daban dake fadin duniya inda za tattauna yadda za a dakile aiyukan laifuka da ake aikatawa da suka hada da damfara ta yanan gizo, da dai sauransu. Batun samar da dabaru da inganta aiyukan tsaro domin bada kariya ga al umma duk suna cikin batutuwa da za a maida hankali akansu a wurin taron. Kuma a yau ne ake saran Babban sifetan yan sandan Najeriya Kayode Adeolu

An shawarci matasa da su bada tasu gudumawa wajen Samar da hadin Kai da zaman lafiya a tsakanin Al umma.

Image
A wani mataki na samar da hadin kai da zaman lafiya a tsakanin matasa kwamandan rundunan tsaro ta operation SAFE HAVEN dake jahar Jos Major Gen. AE Abubakar ya shawarci matasa wadanda suka fito daga jihohin Filatau, Kaduna da jahar Bauchi da sukasance masu gudanar da aiyukan da zaikawo hadin kai dama zaman lafiya a tsakanin al umma. Kwamandan ya bada shawaranne a lokacinda a kammal wasan kwallon kafa wanda rundunan ta shiryawa matasan a filin wasana Rwang Pam dake cikin garin Jos. Kwamandan wanda shugaban ma aikatan rundunan ta SAFE HAVEN Brig. Gen. A A Egbejule ya wakilta yace an shirya da zumar samar da inganceccen zaman lafiya hadin kai dama cigaba a tsakanin rundunan da Al umma. Don haka ya kirayi matasan da su tabbatar sun bada nasu gudumawar wajen samar da zaman lafiya da hadin kai da kuma cigaban jihihin.tare da shawartarsu da sukaucewa duk abinda zaikawo tashin hankali da rashin tuwa a tsakanin jama a.