Posts

Showing posts from December, 2022

Rundunan yan sandan jahar Filato ta dakatar da zirga zirgan mashuna a garuruwan Jos da Bukuru domin gudanar da bikin sabuwar shekara.

Rundunan yan sandan jahar Filato ta dakatar da zirga zirgan mashuna a cikin garin jos da Bukuru a wani mataki na inganta tsaro domin ganin an yi bukukiwar sabuwar shekara lafiya. Sanarwan hakan na kunshena a cikin wata sanarwa da kakakon rundunan yan sandan jahar filato DSP Alfred Alabo ya sanyawa hanu wanda aka rarrabawa manema labarai a Jos. A cikin sanarwan anjiyo kwamishinan yan sandan jahar Folato CP Bartholew N Onyeka ya bada umurnin dakatar da zirga zirgan maahunan wanda acewarsa hakan zaitaimaka wajen ganin anyi bukukuwar sabuwar shekara lafiya. Rundunan ta gargadi mazauna jahar da cewa har yanzufa dokan hana watsa tarsasin wuta dama buga ababe masu kara yananan nan daram saboda haka duk wanda aka kama da yiwa doka karan tsaye zai gamu da fushin hukuma. Kwamishinan ya tabbatarwa mazauna jahar cewa rundunan a shirye take ta kare rayuka dama dukiyoyin al umma fafin jahar baki daya. Ya kuma taya al ummar jahar kurnan bikin sabuwar shekara ta

An shawarci manoma da su maida hankali wajen amfani da inganceccen iri.

Image
An shawarci manoman Auduga da su bukasa noman auduga ta amfanin da inganceccen iri domin samun wadaceccen auduga wanda hakan zai taimaka wajen samar da kudin dama aikinyi a tsakanin matasa. Ko odinatan hukumar inganta fasahar iri a Najeriya Dr Rose Maxwell Gidado ce ta baiyana haka a zantawarta da Jaridar Al Nur a yola. Dr Rose tace noma auduga yana da muhimmanci musamamma wadanda aka inganta iri domin yana dauke da sanadarin kariya daga kwari kuma baya bukatĂ r feshi da yawa sannan yana jibre fari ga kuma samar da ishesheshen auduga. Ta kuma ce a yanzu noma auduga ya taimakawa ta wajenn yin abubuwa masu yawa da suka hada da biyan bukatun manoma auduga da kuma yin amfani da audugan wajen yin sake sake da dai sauransu. Don haka tace manoma bai kamata suyi da wasaba wajen rungumar harkokin noma auduga wanda acewarta hakan zai taimaka wajen bunkasa tattalin arziki kasa baki daya. A bangaren sauran irin da suka hada na shinkafa, masara, sukam ana

An shawarci masu gina makarantun Islamiyoyi da su rinka maida hankalin kan makarantun.

Image
An shawarci masu gina Islamiyoyi da su mada hankali wajen inganta gina islamiyoyi da ma diban malamai masu karantarwa domin inganta karantarwa makarantn Islamiyoyi yadda ya kamata. Shugaba kungiyar Majalisar Islamiyoyi a jahar Adamawa Mallam Muktar Dayyib ne ya bada wannan shawara a zantawarsa da Jaridar Al Nur a yola. Mallam Muktar yace ana fuskantar matsaloli da dama a cikin makarantu Islamiyoyi don haka dole a maida hankali wajen daukan malamai da zasu karantar a makarantun. Acewarsa dai makarantu Islamiyoyi sune ginshikin karantar da yara saboda haka ya zama wajibi a inganta makarantu ta karantarwa da kuma suwaye ne zasu karantar a makarantu. Mallam Dayyib ya kirayi malamai musammanma masu karantar da Islamiyoyi da su sanifa an basu amanan karantar da yarane don haka baikamata suci amanaba. Ya kuma kirayi iyayen yara da suma sukasance suna bada tasu gudumawar ta buyar kudin makarnta yaransu akan lokaci da kuma hada kai da malamai waje

An bukaci yan agaji su kara himma wajen taimakawa al ummah.

Image
An kirayi yan agaji da su kasance masu da a da kuma bin umurnin shugabanni a koda yaushe domin samun cigaba dama inganta ayukan agaji harma da taimakawa al ummah. Alhaji Ibrahim Jalo ne yayi wannan kira a zantawarsa da Jarida Al Nur a lokacin da ake gudanar da horo da akeyiwa yan agaji wanda kungiyar Izala mai shelkwata a jos ta shirya a yola radar gwamnatin jahar Adamawa. Ibrahim Jalo wanda kuma kwamanda ne a wurin boron yace suna gudanar da irin wannan horone daga matakin kananan hukumomi da jahar harma da kasa baki daya. Acewarsa dai suna yin hakane domin horan da yan agajin sanin madafan aiki da kuma yadda zasu gudanar da aiyukansu cikin kwanciyar hankali ba tare da matsaloliba. Don hakqnema ya kirayi yan agaji da sukasance masu biyayya ga shuwagabani domin ganin sun samu nasara a aiyukansu. Ya kuma shawarcesu da suyi amfani da abunda aka koya musu dama fadadashi ga wadanda basu samu damar zuwa ba domin samun cigaban aiyukan agaji yadda ya kamat

An bukaci malamai da su fadada aiyukansu wajen wayarwa matasa kai

An kirayi malamai da su kara fadada wa azuzzukasu zuwa lunguna da sako sako dake fadin jahar Adamawa dama fadakar da matasa dangane da muhimmancin neman ilimin addini dama samar da zaman lafiya a tsakanin al ummah. Hakimin Gombi Alhaji Usman Ibrahim sarkin fada ne yayi wannan kira a lokacinda majalisar addinin musulunci a jahar Adamawa ta shirya taron Da awa a karamar hukumar ta Gombi. Hakimin yace matasa su suke da kaso masu yawa a tsakanin al ummah don haka ya kamata a maida hankali akansu ta wajen nuna masu muhimmancin hadin kai da kuma neman ilimi wanda acewarsa hakan zaitaimaka wajen samar da zaman lafiya maidaurewa. Don haka ya kamata malamai su dukufa wajen Jan hankalin matasan a koda yaushe tare da shawartan iyaye da kuma su hada tasu gudumawar wajen fadakar da matasa dangane da yadda zasu inganta rayuwarsu yadda ta kamata. Ya kuma kirayi masu rike da masarautun gargajiya da suma sukasance masu bada hadin kai wajen wayarwa matasan kai domin ga

An samu hatsarin mota a tsakanin Mayo Belwa da Jada.

An samu hatsarin motoci biyu akan hanyar dake tsakanin karamar hukumar Mayo Belwa da karamar hukumar Jada dake jahar Adamawa a daren litinin da tagabata. Shadar gani da ido Muhammad Sani Jada ya tabbatarwa Jarida Al Nur cewa lamarin ya farune a tsakanin wata motar daukan kaya da kuma karamar mota. Kawo yanzu dai ba asan abunda ya haddasa hatsarinba sai dai anfin daganta yawan hatsari na faruwa sakomakon yawan gudu ko kuma rashin kyaun hanya. A yanzu haka dai mutum dayane aka tabbatar ya samu rauni sakamokon tsarin.

Kungiyar mafarauta NHFSS ta lashi takwabin inganta tsaro a dajuka.

Daga Ibrahim Abubakar yola. A wani mataki na magance matsalar tsaro kungiyar mafarauta da inganta tsaron daji a Najeriya wato NHFSS a takaice shiyar jahar Adamawa ta sha alwashin kauda dukkanin ta addanci a cikin daji baki daya. Kwamandar kunguyar mafarauta wato NHFSS Aisha Bakari Gombi ce ta bayana haka a taron da kungiyar ta gabatar a yola. Kwamandan tace a shirye suke su shiga dajin dake fadin kasan nan domin fatattakan masu aikata lafuka a daji da kuma dakile aiyukansu baki daya. Tace yanzu lokaci yayi da baza a nade hanu a barwa gwamnati komaiba don haka ya kamata al ummah su bada hadin kai da goyon baya domin ganin an cimma nasaran kawo karshen matsalar tsaro baki daya. Ta kuma baiyana cewa kungiyar a ahirye take ta hada kai da dukkanin hukumomin tsaro domin tabbatar da ganin an kare rayuka dama dukiyoyin al ummah. Mai martaba Lamido Adamawa Dr Muhammed Barkindo Aliyu ya yabawa kungiyar mafarautar bisa wannan na miji

Majalisar addinin musulunci a jahar ta gudanar da taron Da awa a karamar hukumar Gombi dĂ ke jahar Adamawa.

Image
Majalisar addinin musulunci a jahar Adamawa ta kudiri aniyar hada kan musulmai dake fadin jahar ta Adamawa baki daya. Shugaban majalisar addinin misuluncin a jahar Adamawa Alhaji Gambo Jika ne ya tabbatar da haka a lokacinda yake jawabi a wurin taron Da awa wanda majalisar ta shiraya a yankin mazabar tsakiya jahar wanda aka gudanar a karamar hukumar Gombi dake jahar ta Adamawa. Alhaji Gambo Jika yace yanzu lokaci yayi da al ummah musulmai zasu kasance tsintsiya madaurinki daya ba tare da nuna banbancin a kidaba wanda acewarsa hakan zai taimaka wajen samun cigaba addinin musuluncin yadda ya kamata. Don hakanema ya kirayi sarakunan gargajiya da sukasance masu basu hadin kai da goyon baya domin ganin sun kai ga nasara wajen hadin kai a tsakanin al ummah musulmai. Ya kuma kiaryi yan siyasa dasu kasance masu basu hadin kai wajen amsa gaiyyata da suke musu domin acewarsa indan suka gaiyaci yan siyasa a wurin tarurrukansu basa halrta illa kalilan daga cikinsu.

Wata kungiyar matasa ta kai ziyara a wata Mujami a a ranan bikin kirsimeti a wani mataki na wanzar da zaman lafiya.

Image
Daga Sani Yarima a Jalingo. Kungiyar matasa mai ragin samar da zakan lafiya a Najeriya wato NGYFPI a takaice shiayr jahar Kaduna ta taya mabiya addinin kirista murnan bikin kirsimeti a mujami ar ECWA dake unguwar Rimi a cikin karamar hukumar Kaduna ta arewa. A jahar ta Kaduna. Ko odinaton kungiyar a shiyar Kaduna Kwamuret Abdulmajid Suleiman Iya baiyana a lokacin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai dangane da ziyaran da suka kaiwa mabiya addinin kirista. Yace sunkai ziyaranne saboda tayasu murnan bikin kirsimeti na wannan shekara. Abdulmajid have zaiyi amfani da wanna dama wajen kiran yan Najeriya da sukasance masu gudanar da dukkanin abunda zai kawo zaman lafiya da ma hadin kai a tsakanin yan Najeriya baki daya. Indama yace wannan nema manufar ziyarar tasu. Ko Odinaton ya kara da ceawa sunyi amfani da wananan ziyarar wajen fadakar da al umma kan kaucwa dukkanin abida yake kawo dumaman yanayi. Shima a zantawarsa da manema labarai Rev,

NAFAN ACADEMY DAKE JAMBUTU

Image
Makarantar NAFAN academy wanda ta zama gwarzuwa wajen bada inganceccen ilimi a bagarori daban daban.

Babban sifeton Najeriya ya nuna alhinsa dangane da mutuwar wata aluya a lagos

Image
Babban sifeton yan sandan Najeriya Usman Alkali Baba ya nuna alhininsa da takaicinsa dangane da mutuwar wata lauya mai suna Omobonle Raheem wanda ake zargin yan sanda ne suka yi sanadiyar mutywarta sakamokon harbinta da akayi a jahar Lagos. Babban sifeton ya baiyana haka ne a wata sanarwa dauke da sanya hanun kakakin runduna yan sandan na kasa CSP Olumuyiwa Adejobi. Babba sifeton ya baiyana lamarin a matsayin abin takacine kuma za and gudanar da bincike dangane da lamarin. Ya kuma jajantawa iyalen marigayiyar da ma abokan arziki dangane da mutuwar lauyar.

Wasu Mazauna Jalingo sun kirayi hukumar zabe da ta samar musu da katin zabe kafin ranan Babban zabe.

Image
Wasu mazauna Cikin grain Jalingo fadar gwamanatin jahar Taraba musammanma wadanda sukayi rijistan katin zabe,kuma ba su samu katinsuba. sun kirayi hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC shiyar jahar Taraba da ta samar musu da katin kafin ranan Babban zabe. Sunyi wannan kirane a lokacinda suka zanta da manema labarai a dai dai lokacin da sukaje karban katinsu amma ba suga nasuba wanda kuma hukumar zabe ta fara rarraba katin zaben ne daga ranan 12-12-2022. Wadanda basu katin nasuba sun baiayana shelkwatan hukumar ne to amma sai akace nasu bai fitoba tukunna, saboda haka su sake dawowa. Daya daga cikin mazauna garin na jalingo mai suna Victoria Baraya tace ta kasance a ofishin hukumar ne domin karban katin ta amma sai aka shaidamata cewa ta dawo ran 6-1-2023. tace kokadan bataji dadiba saboda tanaso tayi amfanin dashi kafin ranan zabe. Wani kuma mai suna Baahir Abba shima ya baiyana rashin jindadinsa da akece nashi katin bai fitoba ahima an

An shawarci ya yan jam iyar APC a jahar Adamawa da su hada kansu domin ganin sun samu nasara a zabe mai zuwa.

Image
An kirayi yan Jam iyar APC a jahar Adamawa da sukasance masu hada Kansu domin siyasa bata "ayi ko a mutu bane" ana siyasa ne domin samun ci gaba da kuma bunkasa dukkanin abunda zai kawo ci gaban al-umma, dama kasa baki daya. Alhaji Sani Jada ne yayi wannan kira a zantawarsa da Jaridar Al Nur a Yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Alhaji Muhammadu Sani Jada yace a daina nuna banbacin kabilanci ko addini a siyasa, wanda acewarsa yin haka ba zai haifarwa kasan Da mai idoba, sai dai ya kawo koma baya a harkokin siyasa da bata zamantakewan Jama'a da dai sauransu. Ya kara dacewa banbance banbace da rashin hadin kai ne yasa Jam iyar APC bata samu nasaraba a zaben shekara da dubu biyu da sha tara da ya gabata. Don haka dolene Jam iyar ta APC ta kasance ta dinke duk dukkanin matsaloli da take ciki domin ganin ta samu nasarar lashe kujeran gwamna a zaben shekara ta dubu biyu da ashirin da uku. Alhaji Sani Jada yace saboda irin aiyukan cigaba da

Rundunan yan sanda a jahar Adamawa ta fatattaki wadanda ake zargi masu garkuwa da mutanene.

A kokarinta na dakile aiyukan da addanci a jahar Adamawa rundunan yan sandan jahar ta Adamawa tayi nasaran tarwatsa wadanda ake zargi masu garkuwa da mutane ne a cikin karamar hukumar Gombi dake jahar Adamawa. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a yola. Sanarwan tace an samu nasaran haka ne biyo bayan bayanai da aka samu cewa wasu mutane da basu wuce biyarba dauke da makamai inda suka kaiwa wani mai suna Musa Muhammed hari wanda a yanzu hakama yana jinya a asibiti sakamokon raunuka da ya samu biyo bayan harinda mutanen suka kai masa. Daga jin bayanin haka ne rundunan batayi da wasaba inda suka halarci inda lamarin ya faru karkaahin jagirancin D P O dake kula da ofishin yan sandan dake karamar hukumar Gombi. Tare da hadin gwiwar mafarauta suka kai dauki inda sukabi kafan wadanda ake zargi da kai harin wanda kuma akayi nasara tarwatsasu tare da hallaka mutane biyu

A yayinda aka fusskanci bukukuwar kirsimeti dana sabuwar shekara hukumar kare haddura a jahar Adamawa ta tura jami anta dari takwas da hamsin domin ganin an kakmala bukukiwar lafiya.

Image
Hukumar kare haddura ta kasa wato FRSC tace ta kimtsa domin bada kariya a lokaci dama bayan bukukuwar kirsimeti dama sabuwar shekara a fadin jahar Adamawa. Kwamandan hukumar a jahar Adamawa Yelwa D Dio ne ya sanar da haka a zantawarsa da mamema labarai a ofishinsa dake yola. Kwamadan Yelwa yace daman an kirkiro hukumar ne domin rage yawaitar haddura da ake samu akan manya da kananan hanyoyi dake fadin kasan nan baki daya. Mr Dio yace kawo yanzu sun tura Jami an hukumar su dari takwas da hamsin a fadin jahar ta Adamawa domin tabbatar da ganin ba a samu hadduraba a lokaci da ma bayan bukukuwar kirsimeti da sabuwar shekara. Kwamandan yace Jami ansu zasu kasance a majami u dama wurin tarukan jama a a wani mataki na kare haddura dama rayukan al ummar. Harwayau kwamandan yace sukanyi amfani da majami u,masallatai, tashoshi harma da kafafen yada labarai domin fadakar da al umma dangane da kula da tuki ababen hawa musammanma akan manyan tituna dake

Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta lashi takwabin ganin an kammala bukukiwar kirsemeti dama sabuwar shekara lafiya.

Image
Rundunan yan sandan jahar Adamawa tace ta baza komarta a dukkanin kanaan hukumomi ashirin da daya dake fadin jahar domin ganin an yi bukukuwar kirisemeti dama sabuwar shekara lafiya ba tare davhatsaniyaba. Rundunan ta bayyana haka ne a wata sanarwa da kakakin rundunan SP Suleiman Yahaya Ngurije ya sanyawa hanu wanda aka rabawa manema labarai a yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. A cikin sanarwan an jiyo kwamishinan yan sandan jahar ta Adamawa C P Sikiru Kayode Akande na umurtan dukkanin Jami an yan sandan dake yankuna harms dana kananan hukumomi da su daura damaran ganin sun saka kafar wanda daya ga duk wanda zaiyiwa doka karan tsaye tare da tabbatar da ganin an kare rayuka dama dukiyoyin al umma a lokaci dama bayan bukukuwar kirisemeti har da sabuwar shekara. Kwamishinan yace tunin rundunan ta kimtsa tsaf domin tura Jami anta a wuraren ibada dama wuraren tarurruka dake fadin jahar. Don haka nema yake tabbatarwa al ummar jahar da sugudanar da lamaransu cikin kwan

Kungiyar yan kasuwar arwacin Najeriya ta yabawa Babban bankin Najeriya .

Image
Kungiyar yan kasuwa na yankin arewacin Najeriya ta yabawa Babban bankin Najeriya bisa sauya dokan kayyade cire kudi gaga Naira dubu dari a mako ga daidaikum jama a zuwa dubu dari biyar a mako a yayinda kamfanoni kuwa daga dubu dari biyar a mako zuwa milyon biyar. Shugaban kungiyar yan ksauwa na yankin arewacin Najeriya Alhaji Muhammed Ibrahim 86 ne ya baiyana haka a zantawarsa da jaridar Al Nur a yola. Alhaji Ibrahim 86 yace Babban bankin na Najeriya yayi dai dai da ya saurari koke koken jama a dangane da lamarin kuma ya janye dokan cire kudin da yasa tunda farko don haka wannan cigabane sosai. Wanda kuma hakan zai bunkasa tattalin arzikin kasa yadda ya kamata. Alhaji Ibrahim yace hakan zai taimakawa kananan yan kasuwa da matsakaitar yan kasuwa samun damar bunkasa kasuwancinsu ba tare da wasu matsaloliba. Don haka nema ya kirayi yan kasuwan da sukasance masu baiwa tsare tsaren gwamnati hadin kai da goyon baya domin ganin ta cimma burinta na bunkasa harkoki

An shawarci mata musammanma wadanda sukayii rijistan katin zabe da suje su karbi katin zabensu.

Image
An kirayi mata musammanma wadanda sukai rijistak katin zabe da suje cibiyar hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa domin karban katin zabensu wanda haka zai basu damar shuwagani da suke so a ranan zabe. Shugaban kungiyar mata musulmai ta tarayya FOMWAN shiyar jahar Adamawa Hajiya Khadija Buba ce ta yi wannan kira a zantawarta da jaridar All Nur a yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Hajiya Khadija Buba tace yana da muhimmanci duk wanda tayi rijstan katin zabe to kada ta yi da wasa wajen kabar katin domin ganin itama ta shiga sahun masu zabe a shekara ta dubu biyu da ashirin da uku. Hajiya Khadija ta shwarci mata da subi dukkanin dokokin da suka dace a wajen karban katin tare da gaggauta karba saboda hukumar zaben ta fara bada katin zaben ne daga watan disemba wanda kuma zata rufe karba katin a ranan ashirin da biyu ga watan janairu shekara ta dubu biyu da ashirin da uku. Ta kirayi matan da kada wasu su rudesu su karbe katun zabensu kada kuma su sayar

Kakakin majalisar dokokin jahar taraba yayi murabus.

Daga Sani Yarima a Jalingo. Rahotanni daga jahar Taraba na baiyana cewa kakakin majalisar dokokin jahar wato Rt Hon Farfesa Joseph Albasu Kunini yayi murabus daga mukaminsa. Kakakin majalisar ya yi murabus dinne a wata wasika da ya aikewa majalisar dokokin jahar a laraban nan. Wasikan wanda mataimakin kakakin majalisar Hamman Adama ya karanta a zauren majalisar wanda kuma shine ya jagoranci zaman majalisar. Inda yace kakakin majalisar yayi murabus din ne bisa radin kansa. Kawo yanzu dai shugaban kwamitin ilimi a majalisar kuma shugaba mai tsawatarwa John Kizito Bonzena wanda yake wakiltan Zing a majalisar shine aka zaba a matsayin sabon kakakin majalisar dokokin jahar ta Taraba. Da yake yiwa maema labarai jawabin Jin kadan da kammala zaman majalisar sabon kakakin majalisar Hon John Kizito Bonzena ya murabus din da kakakin yayi ba zai shafi harkokin siyasar jaharba. Yace duk da cewa Kunini ya yi murabus din ne bisa radin kansa, amman har yanzu sh

Shuhaban kwamitin amintattun kungiyar IPMAN ya taya Alhaji Aminu Abdulkadir Muranan samun sarautar gargajiya.

Image
Shugaban kwamitin amintattu na kungiyar dillalain mai fetir mai zaman kanta ta kasa IPMAN Alhaji Babakano Jada ya taya Alhaji Aminu Abdulkadir murnan samun mukamin saratar Walin Adamawa wanda mai martaba Lamidon Adamawa Dr Muhammadu Barkindo Aliyu Mustafa ya Bashi wanda kuma akayi bikin nadin sarautar a ranan asabat din da tagabata. Alhaji Baba kano Jada yayi adu ar Allah madaukakin sarki ya taya riko ya kuma kare tare da sanya albarka. Ya kuma tabbatar masa da cewa a shirye suke su bashi hadin kai da goyon baya domin ganin ya samu nasaran gudanar da aiyukan cigaban masarautar Fombina. Dama jahar baki days.

An kaddamar da kwamitin neman Zaben Tinubu Ta Shatima a jahar Taraba.

Image
An kaddamar da fara gangamin neman zabe shugaban kasa Bola Ahmed Tinibu da Shatima a karkashin jam iyar A P C a jahar Taraba. Ministan sifiri a Najeriya Alhaji Mu azu Sambo Jaji ne ya jagiranci kaddamar da kwamitin da zasuyi aikin nemana zaben Ahmed Bola Tinibu da Shatima a Jalingo fadar gwamnatin jahar Taraba. Da yake kaddamar da kwamintin Sambo ya kirayesu da suyi aiki tukuru domin hada kan yayan jam iyar ta A P C wanda hakan zai basu damar yin nasara a dukkanin matakai a fadin jahar baki daya. Ministan yace yana mai farin ciki da Allah ya nuna masa wannan rana na kaddamar da kwamitin da za su jagiranci gangamin neman zabe shugaban a jam iyar A P C wato Bola Tinibu da Shatima. Ya kuma baiyana cewa Jam iyar A P C jamiya ce da take da manufa mai kyau da kuma gudanar da aikin cigaban kasa. Don haka nema yake kira ga yan Najeriya da su baiwa jam iyar A P C kuria domin ta cigaba da gudanar da aiyukan cigaba da takeyi. Wasu daga cikin yayan j

An kirayi al umma fulani musammanma wadanda sukayi rijistan katin zabe da suje su karbi katin zabensu.

Image
An kirayi al umma Fulani muasqmmanma wadanda sukayi rijistan katin zabe da suje su karbi katin zabensi domin hakan ne zai basu damar wamda zai cire musu kitse a wuta. Alhaji Sa idu Maikano kuma shugaban matasan Fulani a Najeriya ne yayi wannan kira a zantawarsa da manema labarai a yola. Alhaji Sa idu Maikano yace al umma Fulani suna da kuri a masu yawa saboda haka ya kamata suje su karbi katin su wanda a yanzu haka hukimar zabe mai zaman kanta ta kasa ta cigaba da bayarwa a dukkanin cibiyoyinta dake fadin kasan nan. Alhaji Sa idu yace ya kamata al umma Fulani su sani kuri arsu tana da muhimmanci domin da shine zasu zabi shugaban da sukeso wanda suke ganin zai iya magance masu matsalolinsu. In kuma basu da kuri a to zasu zama yan kallo. Saboda haka ya kamata su gaggauta zuwa cibiyoyin hukumar zaben domin karban katin su wanda hakan zai kare musu mutuncinsu da kuma yancinsu yadda ya kamata. Ya kuma shawarci al umma Fulani musammanma matasa da s

Makarantar gwamnati GSS Numan tayi nasara akan takwaranta na kamfanin Dangode.

Makarantar gwamnati wato GSS Numan ta yi nasarar doke makarantan kamfanin dangote a wani gasar kwallon kafa da aka gudanar a garin numan. Kamfanin Dangote ne ya shirya Gasar kwallon kafar, da zimmar gina kyakkyawar mu’amala tare da gina harkokin wasanni na matasa dake garuruwa dake kewaye da shi. Da yayi jawabi a ranar kammala gasar, shugaban kamfanin Dangote dake Numan, Mista Chinanya Silvail, wanda ya samu wakilcin shugaban sashin ci gaban filaye na kamfanin, Ibrahim Mohammed Doka yace makasudin shirya wannan gasa shi ne domin hada kan al’umma dake kewaya da kamfanin. A cewar shi, wannan ne karo na farko da kamfanin Dangote ke shirya irin wannan gasa na kwallon kafa, kuma zai ci gaba da shirye ire iren wadannan gasa cikin jerin aiyuka da yake gudanarwa. Hakimin garin borrong, cif Lwassam Gadddiel Naina wanda ya wakilci masarautan kasar Mbula a bukin rufe gasar, ya yabawa kamfanin suga na Dangote dashirya wa matasan

Kungiyar Izala ta aurar da marayu ashirin a jahar Adamaww.

An kirayi mawadata da su rinka taimakawa marayu a koda yaushe domin samun fafalan Allah madaukakin sarki da kuma samun dukiya mai albarka dama samun rabao ranana gobe kiyama. Shugaban kungiyar Izala ta kasa Sheik Abdullahi Bala Lau ne ya yi wannan kira a lokacinda ya jagoranci daurin auren marayu ashirin wanda akayi a Babban Masallacin Jumm a dake Daubeli a cikin karamar hukumar yola ta arewa dĂ ke jahar Adamawa. Sheik Abdullahi Bala Lau yace taimakawa maryu yana da mutakan muhimmani da kuma samun dinbin lada daga wurin Allah don haka ya kamata masu hanu da shuni sukasance masu maida hankali wajen taimakawa marayu domin suma su samu walwala a tsakanin al umma. Ya kuma kirayi al umma musulmai sukasance masu hada Kansu da kuma gudanar da adu o i wanzar da zaman lafiya tare da tausayawa juna wanda hakan zai taimaka wajen cigaban addinin musulunci baki daya. Ya kuma shawarci marayu musammanma wadanda aka daura musu auren da sukasance masu tsoron Allah da kum

An kaddaar da fara shirye shiryen aikin hajjin shekara ta dubu biyu da ashirin da uku.

Gwamna Ahmadu Uamaru Fintiri na jahar Adamawa ya kaddakar da fara shirye shirye aikin hajjin shekara ta dubu biyu da ashirin da uku domin bada damar ganin an gudanar da aiki hajji yadda ya kamata ba tare da matsalaba. Gwamnan wanda kakakin majalisar dokokin jahar Adamawa Aminu Iya Abbas ya wakilta yace an kaddamar da fara shirye shirye aikin hajjinne domin baiwa hukumar yin shirye shirye akan lokaci. Ya kuma kirayi al umma musulmai da su baiwa hukumar dama gwamnatin hadin kai da goyon baya domin ganin ba a saku matsalaba a lokacin aikin hajjin na shekara ta 2023. Shima a jawabinsa Babban sakataren hukumar aikin hajji a jahar Adamawa Salihu Abubakar ya godewa gwamna Ahmdu Umaru Fintir bisa goyon baya da ya bayar wajen aikin hajjin shekara ta 2022. Wanda acewarsa an samu nasara sosai a lokacin aikin Hajjin na shekara 2022. Da yake nashi jawabi shugaban hukumar aikin Hajjin a jahar Adamawa Ustas Bappari Umar Kem shima godiyayiwa gwamna bada hadin kai da goyon

An bukaci wadanda sukayi rijistan katin zabe da suje su karbaibi katin zabensu domin su samu damar kada kuri a.

An kirayi al umma musammanma wadanda sukayi rijistan katin zabe ta suje su karbi katinsu wanda hakan ne zai basu damar jefa kuri a a ranan zaben shekara da dubu biyu da ashirin da uku. Jami I mai hulda da jama a na hukumar zaben mai zaman kanta ta kasa shiyar jahar Adamawa Dahiru Jauro ne ya yi wanan kira a lokacin da yake jawabi a wurin taron kungiyar limamai na jahar Adamawa wanda ta shirya a yola. Dahiru Jauro yace akwai mutane da dama wadanda sukayi rijista amman har yanzu basu je sun karbi katunsuba wanda kuma hakan koma bayane musammanma ga su wadanda sukayi rijistan katin zaben. Ya kuma kirayi limamai da suma su bada tasu gudumawar wajen fadakar da al umma dangane da muhimmancin katin zaben domin mallakan katin zaben shine yancinsu. Shima a jawabins malam Muhammadu Umar Zingina kiran limamain yayi da su kasance masu koyi da halayen Annabi Muhammadu (S A W) ta yadda ya gudanar da shugabancinsa ga al ummah. Malam Salihu Dauda Babban limami

Kungayar Arewa Decide ta sha alwashin gain Atiku Abubakar yayi nasra a zaben shekara ta dubu biyu da ashirin da uku.

Kungiyar Arewa Decide ta sha alwashin ganin dan takaran shugaban kasa a karkashin Jam iyar P D P Alhaji Atiku Abubakar ya lashen zaben shugaban kasa a babban zaben shekara ta dubu biyu da ashirin da uku. Kungiya ta baiyana hakane a wani gangamin nuna goyon bayanta ga Atiku wanda aka gudanar a cikin garin Jimeta a karamar hukumar yola ta arewa radar gwamnatin jahar Adamawa. Da yake yiwa manema labarai jawabi ko odinaton kungiyar a jahar Adamawa Ahmed Bello yace sun shiraya wannan gangamin ne domin nuns goyon bayansu ga Alhaji Atiku Abubakar ganin shi dan yankin arewacin Najeriya ne. Don haka suka ga ya kamata su maramasa baya, domin ganin ya samu nasara. Ahmed ya kara da cewa sukam a shirye suke subi dukkanin hanyiyin da suka dace na ganin cewa Alhaji Atiku Abubakar ya kai ga samun nasara cikin kwanciyar hankali ba tare da matsaloliba. Wanda acewarsu Atiku ne zai ceto su ta sama musu aikinyi da kuma magance matsalar tsaro a fadin kasan nan baki daya.

An bukaci yan Najeriya ta su zabi cancĂ nta.

A yayinda aka cigaba da gangĂ min neman zabe mukamai daban daban walau na shugaban kasa ko na yan majalisu tarayya dana jihihi harma dana gwamnoni wanda akeyi lunguna dama sako sako a fadin Najeriya. Wanda hakan yasa aka kirayi yan Najeriya da sukasance maau zaban cancanta a lokacin da sukazo kada kiri unsu. Alhaji BabaKano Jada ne ya yi wannan kira a lokaci da yake zantawa da jaridar Al Nur a yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Alhaji Baba Kano yace yan Najeriya musammanmq yankin arewacin Najeriya su anifa wannan lokaci damace a garesu da su zabi wanda zai kare musu muradunsu dama cigaban yankin don haka kada suyi wa kansu sakiyar da babu ruwa wajen zaban tumun dare. Saboda haka ya kamata su baiwa Alhaji Atiku Abubakar goyon baya domin ya kashi ga samun nasara domin acewarsa shine zai kawo cigaban tattalin arziki kasancewarsa dan kasuwa kuma ya kware a siyasa. Don haka zai magance matsalar tsaro da yake ciwa al umma tuwo a kwarya. Baba Kano ya

An kirayi iyaye da sukasance masu sauke hakkin yaransu.

Dangane da bada inganceccen tarbiya ga yara an kirayi iyaye da cewa sune suke da kaso mafi yawa wajen baiwa yaransu tarbiya. Don haka dolene su tashi tsaye domin sauke hakkin da Allah ya dora musu kan kula da yaran. Shugaban kungiyar Attarahum Foundation a jahar Adamawa Mallam Muktar Dayyib ne ya yi wannan kira a zantawarsa da manema labarai a yola. Mallam Muktar Dayyib yace iyaye susanifa Allah madaukakin sarki zaitambayesu yadda suka tarbiyatar da yaran su domin Amanan yaran ne Allah ya basu. Don haka ashe bai kamata ace iyaye sunyi wasa da tarbiyar yaransunba. Saboda haka su sani yaran suna da hakki akansu kuma dole ne Allah madaukakin sarki za tambayesu hakkin da aka basu. Saboda haka baiga dalilinda yasa iyaye zasu rika yin sakaci da tarbiyar yaransuba. Ya kuma kirayi malamai da sukasance masu wayarwa al umma kai dangane da irin muhimancin tarbiyar yara da kuma illar rashin tarbiyar yaran wanda acewarsa haka zai taimaka wajen samar da inganc

An kirayi Babban bankin Najeriya da yayi la akari da kanaan yan kasuwa kan kayyade kudi da za a iya cirewa a yini.

A cigaba da koke koke da akeyi dangane da yadda Babban bankin Najeriya kayyade yadda dai dai kum mutane dama kakfanoni zasu rinka cirewa a yin ko mako wanda ya kama daga dubu dari zuwa dari biyar wanda hakan yasa kungiyar yan kasuwa a rewacin Najeriya ta nuna damuwarta dangane da lamarin. Shugaban kungiyar yan kasuwa a arewacin Najeriya Alhaji Muhammed Ibrahim 86 ne ya baiyana haka a wata tattaunawa da yayi da jaridar Al Nur a yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Alhaji Muhammed Ibrahim 86 yace Babban bankin na Najeriya baiyi la akari da yan kasuwa dake karkaraba wadanda yawancinsu basu da asusun ajiya a bankuna don haka wannan mataki na Babban bankin Najeriya zai iya nakasa harkokin kasiwancin karkara. Saboda haka ya kamata Babban bankin yasake nazari domin kara yawan kudi da za a cire a yin ko a mako. Alhaji Ibrahim yace ga misali mutum yaje ya sayi saniya a kasuwar karkara to ta yaya zai biya kudin tunda mai saniya bashi da asusun ajiya a banki kai kuma ba aba

Manoma dake yankin baggare sun koka dangane da barnan da kwari ke kusu a ginakai.

Manoma a yankin baggare a cikin karamar hukimar yola ta kudu a jahar Adamawa sun baiyana cewa wasu kwari sun addabi gonakainsu wanda hakan ya sanyasu cikin rashin tabbas na gudanar da harkokin noma a yankin. Manoman sun baiyana hakane a zantawarsu da Jarida Al Nur dangane da halin da suke ciki na matsalat kwarin a gonakain nasu. Hassan Ali Soja manomine kuma shine Ardon Fulanin gwalamba kuma mataimakin shugaban kungiyar Tabbatil Pulaku Jamde Jam Foundation a jahar Adamawa. Yace sun rungimi harkan noman rani amman abunda yake ci musu tuwo a kwarya shie kwari domin suna cinye musu nau o in abundant suka shuka musamma masara. Don haka ya zama wajibi su kirayi gwamnatin jahar dana tarayya da su kawo musu daukin gaggawa domin ceto amfanin ganakain nasu. Mallam Shehu yace a gaskiya suna cikin wani yanayi na bukatar taimako ga wurin gwamnati saboda sun riga sunyi shuka kuma amfanin gona ya fita yadda ya kamata saidai kwari su addabesu sosai. Saboda suna bukatan a tai

An bukaci da mabiya addinin kirista suyi amfani da lokacin bikin kirsimeti wajen adu oin zaman lafiya.

A yayinda aka fusaknci bikin kirsimeti na wannan shekara an kirayi mabiya addinin kirista da suyi amfanin da wannan lokaci wajen kautata halaka da al umma domin samun cigaban zaman lafiya a fadin kasanan baki daya. Shugaban kungitayar kiristoci a Najeriya CAN shiyar jahar Adamawa Rev. Dami Manza ne yayi wannan kira a lokacinda ya tattauna da jaridar Al Nur a yola. Rev. Dami Manza yace wannan lokaci da bikin kirisimeti damace ga mabiya addinin kirista da su sadaukar da Kansu wajen neman yardĂ n Allah Wanda a cewarsa hakan zai taimaka wajen hadin kan mabiya addinin kirstan dama sauran al ummah baki daya. Rev. Manza ya kuma shawarci mabiya addinin kirista da su maida hankali wajen yin adu oi domin neman taimakaon Allah wajen kawo dukkanin karshen matsalar tsaro a fadin kasan nan baki daya. Ya kuma yi fatan Allah yasa a kammal bukukuwar kirisimeti lafiya dama shiga sabiwar shekara lafiya. Tare kuma da kammala zaben shekara ta dubu biyu da ashirin da uku cikin

Kungiyar masu P O S a jahar Adamawa sun koka kan matakin Babban bĂ nkin Najeriya na kayyade kudin da za a cire a rana,

Kungiya ma aikatan P O S a jahar Adamawa sun koka dangane da aniyar Babban bankin Najeriya kan kayyade kudin da daidaikun jama a ko kamfani zasu iya cire a yin zuwa mako, dai daikun mutane suna iya cire dubu ashirn a yini sai kuma kamfani zai iya cire dubu dari biyar kacal a mako lamarinda ya haifar da maida martani daban daban. Shugaban masu P O S a jahar Adamawa Alhaji Auwal Usman shugaban kamfanin Auwalus Business Concept ne yabaiyana koken nasu a zantawarsa da jaridar Al Nur a yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Alhaji Auwal yace basuji dadin wannan lamariba ko kadan don haka nema yake kira ga Babban bankin Najeriya da ya sauya wannan tunani nashi ya duba irin yana yi da ake ciki na wahalar rayuwa. Domin wanan tsari zai sake jafa mutane cikin mawuyacin hali musamman ma su masu aikin P O S wĂ nda kuma zai shafesu ta fannoni daban daban. Auwal kuma kirayi wakilain al umma musammanma yan majlisu da su taimaka su takawa Babban bankin na Najeriya birki dangane d

An bukaci Babban bankin Najeriua ya sausauto daga tsarin da ya fitar na kaiyade cire kudi.

Anja hankalin Babban baniin Najeriya da ya duba tsarin nan da ya fitar na kayyade cire kudi ga daidaikum jama a dama kamfani domin baiwa masu hada hada kudi damar inganta kasuwancinsu. Shugaban kamfanin NFAN a jahar Adamawa Alhaji Adamu Jingi ne yayi wannan kira a lokacin da yake zantawa da jaridar All Nur a yola. Alhaji Adamu yace kaiyade cire kudin zai shafi aiyukansu sosai saboda haka ya kamata babban bankin yayi la akari da yadda kamfanonin ke gudanar da aiyukansu da kuma yadda suke mu amaoa da kudi. A vwar Jingin dai suna sayan kayakin buga ruwa da. kudade masu yawa don haka akwai bukatan ayiwa kamfanonin rangwame ta yadda zasu gudanar da aiyukansu yadda ya kamata. Ya kuma kirayi gwamnati da ta yi dukkanin maiyiwa domin samar wa masu kamfanini hanyoyin da zasu fadada aiyukansu ba wai kaiyade musu abunda zasu cire a asusun su na bankunaba. A cewarsa dai samawa kamfononin wadacen kudi zaitaimaka wajen samar da aikikyi musammanma a tsaka

Kungiyar Tabbutal Pulaku Jamde Jam ta sha alwaahin kawo karshen rikiici a tsakanin manoma damakiyaya a jahat Adamawa.

Kunhuyar Tabbutal Pulaku Jamda Jam Foundation dake jahar Adamawa ta kudiri aniyar kawo karshen rikici a tsakanin manoma da makiyaya fadin jahar Adamawa baki daya. Mataimakin shugaban kungiyar Tabbutal Pulaku Jamde Jam Foundation a jahar Adamawa kuma Ardo Fulanin Gwalamba Hassan Ali Soja ne ya bayana haka a likacin da take zantawa da jaridar Al Nur a yola. Hassan Ali Soja yace ko shakka babu zasuyi dukkanin abinda ya dace domin ganin an magance duo wani rikici a tsakanin manoma da makiyaya domin samun damar bunksa harkokin noma a fadi jahar dama kasa baki daya. Don haka nema ya kirayi manoma da makiyaya da su sanifa su yan uwan junane saboda haka sukasance masu hada Kansu a koda yaishe domin ganin rikici a tsakanin manoma da makiyaya ya zama tarihi. Hassan ya kuma kara da cewa yanzu haka suna iya kokarin ganin sun samar da burtiloli domin baiwa dabbobin hanya kamar yadda gwamnatin tarayya ta bukaci haka. Da wanna nema yake shawartan manoma da makiyaya da su ba

Gidajen maifetur na NNPC mega ne kawai ake samun maifetur a jahar Taraba.

Daga Sani Yarima Jalingo. Rahotanni daga jahar Taraba sun nuna cewa a kawo yanzu gidajen mai NNPC Mega ne kawai ke sayar da mai fetur akan nera dari da tamanin da tara kamar yadda gwamnati ta kaiyade a kowace lita.a yayindakasuwar bayan fage kuwa ana sayar da kowace lita akan nera dari biyu da hamsin zuwa da sittin. Matuka matoci a fadar gwamnati jahar Taraba wato Jalingo sun koka da yadda ake samun karancin mai fetur a fadar jahar lamarin da suka kira da baidaceba. Wasu da suka zantada manema labarai sun baiyama rashim jin dadi dangane da faruwar lamarin wanda kuma ya sanyasu cikin wahala rayuwa. Rahoto ya nuna cewa gidan main din NNPC ne ka wai ke sayar da mai a yanzu sauran gidajen mai dinkam a rufe suke. A yayinda wasu matuka matocin sun kirayi gwamnatin tarayya da tayi dukkanin mai yiwa domin kawo karshen matsalar . Mr Mark Anthony wanda manajane a gidan mai na NNPC ya tabbatar al ummar jahar cewa gidan mai din sai wadadar da mai sai dai sukasance m

Kungiyar hadakan mabukata na musamman ta koka dagane da yadda ba adamawa dasu a gwamnatin jahar Adamawa.

Kingiyar hadaka na abukata na musamman a jahar Adamawa sun koka da yadda gwamnatin ke nuna musu wariya a harkokin gwamnati duk da cewa suma suna da irin nasu gumawar da zasu iya bayarwa na cigaban jahar. Shugabna hadakar kunhiya a jahar Adamawa Injiniya Sani Sabo ne ya baiyan haka a wajen wani taro wanda hukukmar raya kasa da kasa na kasar Amurka wato USAID ta shirya a wani mataki na ranan manukata na musamman ta duniya mai taken inganta tare da dina nunawa mabukata na musamman wariya anan yola. Sani Sabo yace gwamnatin jahar tayi burus da su wajen daukansu aiki harma da kula da walwalansu wanda acewarsa suma suna da gudumawa da zasu iya nayarwa wajen cigaban jahar harma da tattalin arziki. a jahar dama kasa baki daya. Ya kuma godewa hukumar ta USAID bisa shirya wannan taron domin tabbatar da cewa mabukata na musamman za a iya damawa dasu a harkokin duniya baki daya. Shugabar tawagan jahar Adamawa a wajen taron Hajiya Maryam Dikko race ma

Yan takaran gwamnoni sun sanya hanu kan yarjejeniyar zaman lafiya a jahar Adamawa.

An ja hankalin yan takaran kujeran gwamna dake jahar Adamawa da su tabbatar da aiwatar da zaben 2023 cikin zaman lafiya. Kwamishina hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta INEC, na jahar Adamawa, Hudu Yunusa Ari ne ya yi wannan jan hankali yayan zaman rattaba hannu da yan yakaran suka yi na yarjejeniyar zaman lafiya yayin gudanar da harkokin siyasa a Jihar. An dai gudanar da taron sanya haunne a otel na Madugu Rockview, dake nan yola.wanda kuma an yi hakan ne domin samun tabbacin aiwatar da zaben gwamnan jahar da ke tafe a shekara ta 2023 cikin zaman lafiya. Kwamishnan hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta INEC, na jahar Adamawa, Hudu Yunusa Ari yace a ko da yaushe tashe tashen hankali na yi wa harkokin aiwatar da zabuka masu inganci barazana, shi yasa ake bukatan yan takaran su ba da tabbacin samun zaman lafiya ta hanyar rattaba hannu kan wannan yarjejeniyar zaman lafiya. Hudu ya kuma bukace yan takaran da kowa ya nuna amincewar shi ta hanyar ratt

Gwamnatin jahar Adamawa tace tana cigaba da wayarwa al ummah kai dangane da illar cin zarafin biladama.

Gwamnatin jahar Adamawa na cigaba da kokarin wayar da kan al’ummar dangane illar cin zarafin jinsi wato GBV. Kwamishiniyar ma’aiakatar harkokin mata da ci gaban more rayuwa, Misis Lami Patrick ce ta baiyana haka yayin wani zaman tattaunawa kan batun da ya mamaye duniya mai taken KAWO KARSHEN CIN ZARAFIN MATA DA YARA MATA KANANA, domin kaddamar da ranaku 16 na gagwarmaya a Jahar Adamawa, hukumar ci gaban raya kasa da kasa ta kasar Amurka. USAID ce ta shirya a birnin Yola, fadar jahar. Komishiniyar ma’aikatar harkokin mata da ci gaban more rayuwa, Misis Lami Patrick wanda ta samu wakilci jami’in ofishin bada kariya na ma’aiakatar, Hassan Aliyu yayin tattaunawar tace, a kokarin gwamnatin jahar na kawo karshen cin zarafin jinsi a jahar, ta samar da wani cibiyar kai koke, wato one stop referral centre, kari kan wadanda take da su a fadin jahar. Komishiniyar tace, ma’aikatar ta ziyarci kananan hukumomi tara daga cikin ashirin da daya da ake da su domin wayar wa al’umma kai

An gargadi matasa kan bangan siyasa.

A yayinda ana cikin lokacin guguwar siyasa an kirayi matasa da su nisanta kansu da bangan siyasa kuma kar su bari ayi amfani da su wajen cin zarafin wani. Shugaban majalisar malamai na kungiyar Izala mai shelkwata a Jos shiyar jahar Adamawa Sheik Kusa Abdullahi ne ya baiyanan haka a zantawarsa da manema labarai a yola. Sheik Musa Abdullahi yace matasan su sanifa sune kashi bayan al umma sanan kuma sune ahuwagabanin gobe don haka kar su bari ayi amfani dasu wajen karya darajansu a idon al umma. Suma iyaye ya shawarcesu da su kasance masu baiwa yaransu iganceccen tarbiya dama ilimi na addini da na zamani kasancewa iyaye sune suke da mujimiyar gudumawa da zasu bayar wajen tarbiyar yara. Suma yan siyasn ya kirasu da kada suyi amfani da matsan wajen kowowa zaman lafiya barazana musammanma a wannan lokaci na gangamin yakin neman zabe da yake gudana afdin Najeriya. Ya kirayi yan Najeriya da su cigaba da yin adu o i domin ganin an kammala Babban zaben shekar ta dubu biy

An kirayi gwamnatin jahar Taraba da ta baiwa bangaren wasanni muhimmacin.

Daga Sani Yarima Jalingo. A yayinda aka kamala gasar kwallon kafa na Delta National Sport Festival an kirayi gwamnatin jahar Taraba da ta baiwa sashin wasanni muhimmaci domin samun cigaban harkokin wasanni a fadin jahar. Wasu yan wasan kwllon kafa wato Mr Joseph Yohana, Jerry Jermiah da magiyin bayan wasanni Isa Bilal a zantawarsu da manema labarai a Jalingo dangane da kammala wasanin Delta National sports Festival wanda aka gudanar a Asaba fadar gwamnatin jahar. Mutanen dai sun baiyana rashin jin dadinsu dangane da yadda gwamnatin jahar ta Taraba ta nuna halin ko inkula da bangaren wasanni da matasa a fadin jahar. A inda sukce gwamnatin tsohon gwamnan jahar ta Taraba wato Rev. Jolly Nyame ta taka rawan gani wajen inganta sashin wasanni a jahar, wanda hakan yasama filin wasanni jahar yana daya daga cikin wadanda skayi fice a fadin Najeriya. Saboda haka nema suke zargin gwamnati maici a yanzu da rashin katabus a bangaren wasanni tun daga tsofuwar

Akalla mata darine zasu amfana da aikin fida na cutar yoyon fitsari a jahar Bauchi.

A kalla mata darin ne wadanda ke dauke da cutar yoyon fitsari ne suka amfana da aikin fida cutar a cibiyar kula da cutar ta yoyon fitsari ta kasa dake Ningi a jahar Bauchi, Hukumar raya yankin arewa masau gabas tare hadin gwiwar kungiyar dĂ ke taimakawa domin yaki da cutar wato VVF ne suka kaddamar dayin jinyawa wadanda ke dauke da cutar yoyon fitsrin kauta a jahar Bauchi wanda kuma za a tadada aikin a yankin na arewa masau gabas baki daya. Da yake kaddamar da fara aikin kwamishinan kiwon lafiyar a jahar Bauchi Dr Sabir Ahmed wanda darektan kiwon lafiya a jahar Bauchi Robeson Yusuf ya wakilta ya godewa hukumar raya arewa masau gabas da takwaranta ta VVF bisa kokarinsu na taimakawa gwamnatin jahar Bauchi domin kula da lafiya al umma jahar. Yace wanna taimako yazo a daidai don kuwa akwai mata dawa wadanda ke dauke da cutar ta yoyon fitsari amman rashin kudi ya hanasu zuwa asibiti domin yi musu jinya. Saboda haka yana ganin mata da dama zasu amfana da wannan ta

Rundunan yan sanda a jahar Adamawa ta ceto mutene hudu tare da tarwatsa maboyar masu garkuwa da mutane a tsaunin dutsen mboi dake cikin karamar hukumar Song a jahar Adamawa.

Rundunan yan sandan jahar Adamawa tayi nasaran ceto mutane hudu tare da tarwatsa maboyar yan ta adda da suka addabi yankin mboi dake ciki karamar hukumar Song a jahar Adamawa. Kakain rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanar da ya fitar wanda aka rabawa manema labarai a yola. Sanarwan tace rundunan ta gano wayoyin hanu, sarka, bargo, da dai sauransu, a maboyar bata garin a tsaunin dutsen mboi dake cikin karamar hukumar ta Song a jahar Adamawa. Sanarwa tacigaba da cewa ofishin yan sandan dake gundumar Song tare da hadin gwiwar mafarauta ne aka samu nasaran tarwatsa gungun yan ta addan. Kuma an dauki matakin haka ne biyo bayan rahoton da ake samu na ywan sace sacen shanu, garkuwa da mutane, fashi da makami, wanda hakan yasa Jami an yan sandan yin arangama da wadanda ake zargi masu garkuwa da mutane ne wanda kuma sun gudu da raunin harbin bindiga a jikinsu. Kwamishinan yan sanda

An ja hankalin yan majalisar dokokin jahar Taraba da suyi watsi da kudirin dokan da gwamnan jahar ke kokari kai majalisar.

Daga Sani Yarima Jalingo Dan majalisar wakilai tarayara Najeriya mai wakiltan kananan hukumomin wukari da ibi a majalisar wakilain Najeriya. Hon. Danjuma Shiddi ya zargin gwamnan jahar Taraba Darius Ishaku da shirin kaiwa majalisar dokokin jahar kudirin doka da zai kawowa yan jarida nakasu lamarinda ya kira da yiwa damokiradiya karan tsaye, Shiddi wanda akafi sani da Dnji s s ne ya baiyana haka a loakcinda yake amsa tambayoyi daga manema labarai a Jalingo fadar gwamnatin jahar Taraba. A cewarsa tun daga randa yaji cewa gwamnan na yunkuri tuwa majalisar dokokin jahar kudirin dokan shine mutum na farko da ya fara Jan hankalin yan Najeriya da kada su amince da wannan doka da gwamnan ke kokarin kaiwa majalisar domin yin haka ba damokiradiyabace. Ina mai shaida muku cewa ba abida gwamna yakeso yayi illa gurgunta aikin jarida a fadin jahar Wanda kuma wannan bacigaban domokiradiya bane. Don hakanema ya kirayi takwarorinsa a majalisar dokokin jahar da suyi

AN JA HANKALIN MANOMA WAJEN YIN ADANAN KAYAKIN ABINCI.

An kirayia manoma da su maida hankali wajen yadda zasuyi ajiya kayakin da suka noma domin kaucewa abunda zai taba lafiyar al ummah. Alhaji Adamu Jingi ne yaiyi wannan kira a zantawarsa da jaridar Al Nur a yola radar gwamnatin jahar Adamawa. Alhaji Adamu yace dazaran manomi ya kammala aikin gonarsa to yayi amfani da dabaruka da suka kamata wajen addana kayakin gonarsa. A cewarsa dai akwai Leda na musamman wanda mutum zai iya Adana kayakin nomansa ba tare da yayi amfani da sanadarin maganiba. Jingi yace yin amfani da sanadarin magani yana haifar da matsaloli musammanma a bangaren lafiya don haka ya kamata al umma sukasance masuyin taka tsantsan wajen ajiyar kayakin noma. Ya kuma kiayi manoma da su kara kaimi wajen rungumar harkokin noma domin bunkasa abinci a fadin jahar dama kasa baki daya. Harwayau Adamu Jingi ya kirayi yan Najeriya da sukasance masu hada Kansu domin yin aiki kafada da kafada domin samun cigaban kasan nan baki daya. Tare da yin adu o i domin neman

An shawarci matasa su daina furta kalamain batanci a shafukan sada zumunta.

An shawarci matasa musammana wadanda ke amfani da dandalin sada zumunta da su kasance masu wallafa abunda zai amfani Al umma su kuma kaucewa duk wasu kalamain batanci a shafukan sada zununta. Alhaji Salihu Baba Ahmed ne ya bada wannan shawara a zantawarsa da jaridar Al nur a yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Salihu Baba Ahmed yace ba daidaibane a rinka furta kalamain batanci akan wasu wai da sunan yancin fadin albarkacin baki domin shi wanda akayiwa batanci shima yana da yanci, saboda haka al ummah su nisanta kansu da cin zarafin wasu. Ya kuma kirayi iyaye da suma su bada tasu gudumawar wajen Jan hankalin yaransu domin ganin ba a samu irin wadanan matsalaba. Tare da kiran shuwagabanin musammanma wadanda lamarin ya shafa sukasance masu hakuri da yafiya domin samun cigaban zaman lafiya. Don haka nema Salihu Baba Ahmed ya yabawa uwar gidan shugabĂ n kasa Aisha Buhari bisa yafiya da tayiwa matashinan Aminu Muhammed biyo baya cin zarafin ta da yayi a shafuka sada zumunta wanda acew
Barkanku da zuwa wannan shafin labaru